Dakarun Sojin Najeriya Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa da Mutane a Zamfara
Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta a Arewa maso Yammacin ƙasar sun daƙile yunƙurin garkuwa da mutane da ƴan ta’adda suka yi a yankuna daban-daban na Jihar Zamfara, inda suka kuɓutar da fararen hula daga hannun maharan.
A ranar 17 ga watan Agustan 2026, dakarun sun kai ɗauki bayan samun rahoton sace mutane a kan hanyar Gurusu zuwa Anka.
Rundunar ta ce sojojin sun bi sahun maharan cikin gaggawa, lamarin da ya tilasta musu watsar da waɗanda suka yi garkuwa da su tare da tserewa.
Read Also:
An ceto mutum bakwai da suka haɗa da mata huɗu da yara uku ba tare da sun samu rauni ba. Haka kuma a Karamar Hukumar Tsafe, dakarun sun mayar da martani bayan samun bayanan cewa ƴan ta’adda na ƙoƙarin yin garkuwa da matafiya a kusa da ƙauyen Magazu.
Bayan artabu tsakanin ɓangarorin biyu, maharan sun tsere zuwa cikin daji yayin da aka kuɓutar da waɗanda suka kama.
Wasu daga cikin waɗanda aka ceto sun samu raunukan harbin bindiga, kuma an garzaya da su asibiti domin samun kulawar likitoci. Rundunar ta ce dakarunta za su ci gaba da matsa wa ƴan ta’adda lamba domin kare rayuka da dukiyoyin jama’a a yankin.












