Home Labarai Dakarun Sojin Najeriya Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa da Mutane a Zamfara

Dakarun Sojin Najeriya Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa da Mutane a Zamfara

Rundunar Soji

Dakarun Sojin Najeriya Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa da Mutane a Zamfara

 

Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta a Arewa maso Yammacin ƙasar sun daƙile yunƙurin garkuwa da mutane da ƴan ta’adda suka yi a yankuna daban-daban na Jihar Zamfara, inda suka kuɓutar da fararen hula daga hannun maharan.

A ranar 17 ga watan Agustan 2026, dakarun sun kai ɗauki bayan samun rahoton sace mutane a kan hanyar Gurusu zuwa Anka.

Rundunar ta ce sojojin sun bi sahun maharan cikin gaggawa, lamarin da ya tilasta musu watsar da waɗanda suka yi garkuwa da su tare da tserewa.

An ceto mutum bakwai da suka haɗa da mata huɗu da yara uku ba tare da sun samu rauni ba. Haka kuma a Karamar Hukumar Tsafe, dakarun sun mayar da martani bayan samun bayanan cewa ƴan ta’adda na ƙoƙarin yin garkuwa da matafiya a kusa da ƙauyen Magazu.

Bayan artabu tsakanin ɓangarorin biyu, maharan sun tsere zuwa cikin daji yayin da aka kuɓutar da waɗanda suka kama.

Wasu daga cikin waɗanda aka ceto sun samu raunukan harbin bindiga, kuma an garzaya da su asibiti domin samun kulawar likitoci. Rundunar ta ce dakarunta za su ci gaba da matsa wa ƴan ta’adda lamba domin kare rayuka da dukiyoyin jama’a a yankin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Ƴan Sandan Legas Sun Kama Mutum 4 da Ake Zargi da Fashin Daji, Sun Kwato Wayoyin Hannu 25, Kwamfutoci da Kayan Ado na ZinareRundunar Sojin Ruwa Ta Rusa Wuraren Tace Mai Ba bisa Ka’ida Ba, Ta Kwato Lita 350 na AGO a Rivers2027: Yahaya Bello Ya Tara Masu Daidaita Ayyuka na A4A a Arewa ta Tsakiya Domin sake Zaban TinubuSojoji Sun Kama Mutum 2 da ake Zargi da Taimakawa Ƴan Ta’adda, Sun Kwace Kayayyakin Babur a YobePDP Ta Yi Gargadi Kan Zargin Tattara Katunan Zabe PVC da Bayanan Asusun Banki a GombeRundunar Sojojin Najeriya ta Sauya Manyan Janarori Zuwa Muhimman Mukamai na Aiki da DabaruHukumar INEC za ta ƙaddamar da Na’urar Bibiyar shirye-shiryen Zaɓen 2027 kai TsayeDaliban Tallafin Horarwa na Prnigeria Sun Ziyarci Emirate FM, Sun Samu Kyawawan Bayani Kan Watsa Labarai na DijitalNSCIA ta yi Allah Wadai da Nuna Bambancin Addini a Ci gaba da Tsare El-RufaiSarkin Ilorin Ya Yaba da Tallafin Horarwa na PRNigeria Wajen Shirya Masu Watsa Labarai na Nan GabaNDLEA Ta Kama Mai Safarar Hodar Iblis da ake Zargi da Laifi Akan Jigilar Kaya a Saudiyya, ta Kuma Kama Kwayoyi Masu Yaduwa Sama Da Miliyan 2Gwamnatin Tarayya ta Yaba da N5.41 Trillion da Kwastam ta Tara, Ta Nemi a bi Ka'idojin Duniya Hukumar Kwastam Ta Naɗa DCG, ACG 5, ta yi Nazarin Yadda aka Samu Kuɗin Shiga2027: HURIWA Ta Bukaci Ƴan Sanda da su Gurfanar da Ƴan Siyasa Kan Zargin Kalamai Masu Tada HankaliSojoji Sun Tarwatsa Maboyar Ƴan Ta'adda, Sun Kwace Bindigogin AK-47 a Sokoto 
X whatsapp