Home Labarai Dakarun Sojin Najeriya Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa da Mutane a Zamfara

Dakarun Sojin Najeriya Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa da Mutane a Zamfara

Rundunar Soji

Dakarun Sojin Najeriya Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa da Mutane a Zamfara

 

Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta a Arewa maso Yammacin ƙasar sun daƙile yunƙurin garkuwa da mutane da ƴan ta’adda suka yi a yankuna daban-daban na Jihar Zamfara, inda suka kuɓutar da fararen hula daga hannun maharan.

A ranar 17 ga watan Agustan 2026, dakarun sun kai ɗauki bayan samun rahoton sace mutane a kan hanyar Gurusu zuwa Anka.

Rundunar ta ce sojojin sun bi sahun maharan cikin gaggawa, lamarin da ya tilasta musu watsar da waɗanda suka yi garkuwa da su tare da tserewa.

An ceto mutum bakwai da suka haɗa da mata huɗu da yara uku ba tare da sun samu rauni ba. Haka kuma a Karamar Hukumar Tsafe, dakarun sun mayar da martani bayan samun bayanan cewa ƴan ta’adda na ƙoƙarin yin garkuwa da matafiya a kusa da ƙauyen Magazu.

Bayan artabu tsakanin ɓangarorin biyu, maharan sun tsere zuwa cikin daji yayin da aka kuɓutar da waɗanda suka kama.

Wasu daga cikin waɗanda aka ceto sun samu raunukan harbin bindiga, kuma an garzaya da su asibiti domin samun kulawar likitoci. Rundunar ta ce dakarunta za su ci gaba da matsa wa ƴan ta’adda lamba domin kare rayuka da dukiyoyin jama’a a yankin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Anambara: Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'addan IPOB/ESN, Sun Kwato MakamaiHukumar Kwastam ta Kano ta Mika Magungunan da ba a yi wa Rijista ba ga NAFDAC, ta Kuma yi Alƙawarin Tsaurara Matakan Aiki.Operation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Kawar da 'Yan Ta'adda 36 a BornoFamadewa, Ribadu da Shirin Tsaron Kwanaki 90: Yadda YAShuaib ya Binciki Sanarwar OnanugaLabarin NIPSS Ya Bayyana Cin Zarafin Babban Jami'in Sojan Ruwa, Rear Admiral AA MustaphaƊaliban PRNigeria Sun Yaba da Gyare-Gyaren FRSC, Sun Nemi Ƙarin Ƙarfafa Sadarwa Kan Tsaron HanyaYadda Dalibai 4 Almajirai Suka Mutu Bayan Cin Kife da Ake Zargi da Guba a KanoSojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Sace a Dajin KatsinaTinubu Ya Nada Abel Enitan A Matsayin Sabon Shugaban Ma'aikatan TarayyaRundunar Sojin Ruwan Najeriya ta Ceto Mutane 22 Daga Hannun Ƴan Fashin Teku Kimanin Malamai 200 ne Suka bar Jami'ar KASU - ASUUHukumar EFCC ta Gurfanar da Mutumin da ake Zargi da Damfarar Maniyyata Aikin HajjiKashi 40 Cikin 100 Kawai na Cibiyoyin Kiwon Lafiya a Duniya ke da Tsabta - MDDDakarun Sojin Najeriya Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa da Mutane a Zamfara
X whatsapp