Home Taska Kashi 40 Cikin 100 Kawai na Cibiyoyin Kiwon Lafiya a Duniya ke...

Kashi 40 Cikin 100 Kawai na Cibiyoyin Kiwon Lafiya a Duniya ke da Tsabta – MDD

Kashi 40 Cikin 100 Kawai na Cibiyoyin Kiwon Lafiya a Duniya ke da Tsabta – MDD

 

Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) ta ce kashi 40 cikin 100 ne kawai na cibiyoyin kiwon lafiya a duniya ke da banɗakuna masu tsabta da sauran muhimman kayayyakin tsafta da suka dace da marasa lafiya da ma’aikatan lafiya.

A cikin wani rahoto da Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) da UNICEF suka fitar, an nuna cewa kashi 11 cikin 100 na cibiyoyin kiwon lafiya ba su da wata hidimar tsafta kwata-kwata, lamarin da ke shafar kusan mutum miliyan 936 a faɗin duniya.

Rahoton ya kuma bayyana cewa akwai babban bambanci tsakanin yankuna, inda kashi 23 cikin 100 ne kawai na asibitocin da ke yankin Afirka ta kudu da Sahara ke da ingantattun ayyukan tsafta, idan aka kwatanta da kashi 55 cikin 100 a yankunan Tsakiya da Kudancin Asiya.

Baya ga tsafta, rahoton ya ce kashi 85 cikin 100 na cibiyoyin kiwon lafiya suna da wadataccen ruwa, amma ƙasa da kashi 60 cikin 100 ne suka cika ƙa’idojin tsaftace muhalli da hana yaɗuwar cututtuka, musamman a ƙasashe masu ƙarancin ci gaba

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Anambara: Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'addan IPOB/ESN, Sun Kwato MakamaiHukumar Kwastam ta Kano ta Mika Magungunan da ba a yi wa Rijista ba ga NAFDAC, ta Kuma yi Alƙawarin Tsaurara Matakan Aiki.Operation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Kawar da 'Yan Ta'adda 36 a BornoFamadewa, Ribadu da Shirin Tsaron Kwanaki 90: Yadda YAShuaib ya Binciki Sanarwar OnanugaLabarin NIPSS Ya Bayyana Cin Zarafin Babban Jami'in Sojan Ruwa, Rear Admiral AA MustaphaƊaliban PRNigeria Sun Yaba da Gyare-Gyaren FRSC, Sun Nemi Ƙarin Ƙarfafa Sadarwa Kan Tsaron HanyaYadda Dalibai 4 Almajirai Suka Mutu Bayan Cin Kife da Ake Zargi da Guba a KanoSojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Sace a Dajin KatsinaTinubu Ya Nada Abel Enitan A Matsayin Sabon Shugaban Ma'aikatan TarayyaRundunar Sojin Ruwan Najeriya ta Ceto Mutane 22 Daga Hannun Ƴan Fashin Teku Kimanin Malamai 200 ne Suka bar Jami'ar KASU - ASUUHukumar EFCC ta Gurfanar da Mutumin da ake Zargi da Damfarar Maniyyata Aikin HajjiKashi 40 Cikin 100 Kawai na Cibiyoyin Kiwon Lafiya a Duniya ke da Tsabta - MDDDakarun Sojin Najeriya Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa da Mutane a Zamfara
X whatsapp