Home Taska Hukumar EFCC ta Gurfanar da Mutumin da ake Zargi da Damfarar Maniyyata...

Hukumar EFCC ta Gurfanar da Mutumin da ake Zargi da Damfarar Maniyyata Aikin Hajji

Court

Hukumar EFCC ta Gurfanar da Mutumin da ake Zargi da Damfarar Maniyyata Aikin Hajji

 

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa a Najeriya EFCC ta gurfanar da wani mutum a gaban wata babbar kotun jihar Oyo bisa zargin shi da damfarar maniyyata ikin hajji naira miliyan 56.4.

An gurfanar da mutumin ne kan zarge-zarge 57 wadanda ke da alaƙa da fashi da kuma yaudara.

Hukumar ta lissafo sunayen wasu mutane 10 wadanda ta ce mutumin da take zargi ya damfara.

Bayanin shari’ar da EFCC ta shigar ya nuna cewa mutumin ya karɓi kuɗin naira miliyan 56,491,000 daga mutane daga watan Nuwamban 2022 zuwa watan Yulin 2024.

Mutumin ya riƙa shaida wa mutanen da yake karɓar kudi daga wurin su cewa shi jami’in hukumar kula da mahajjata ne ta jihar Kaduna.

EFCC ta ce ya karɓi kuɗaɗen a hannunsu ne bisa hujjar cewa zai taimaka musu wajen tsara tafiyarsu zuwa aikin hajjin shekarar 2023.

Hukumar ta ƙara da cewa mutumin ya ba su rasiɗin shaidar biyan kuɗi na ƙarya daga jihar Kaduna da kuma ƙasar Saudiyya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Anambara: Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'addan IPOB/ESN, Sun Kwato MakamaiHukumar Kwastam ta Kano ta Mika Magungunan da ba a yi wa Rijista ba ga NAFDAC, ta Kuma yi Alƙawarin Tsaurara Matakan Aiki.Operation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Kawar da 'Yan Ta'adda 36 a BornoFamadewa, Ribadu da Shirin Tsaron Kwanaki 90: Yadda YAShuaib ya Binciki Sanarwar OnanugaLabarin NIPSS Ya Bayyana Cin Zarafin Babban Jami'in Sojan Ruwa, Rear Admiral AA MustaphaƊaliban PRNigeria Sun Yaba da Gyare-Gyaren FRSC, Sun Nemi Ƙarin Ƙarfafa Sadarwa Kan Tsaron HanyaYadda Dalibai 4 Almajirai Suka Mutu Bayan Cin Kife da Ake Zargi da Guba a KanoSojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Sace a Dajin KatsinaTinubu Ya Nada Abel Enitan A Matsayin Sabon Shugaban Ma'aikatan TarayyaRundunar Sojin Ruwan Najeriya ta Ceto Mutane 22 Daga Hannun Ƴan Fashin Teku Kimanin Malamai 200 ne Suka bar Jami'ar KASU - ASUUHukumar EFCC ta Gurfanar da Mutumin da ake Zargi da Damfarar Maniyyata Aikin HajjiKashi 40 Cikin 100 Kawai na Cibiyoyin Kiwon Lafiya a Duniya ke da Tsabta - MDDDakarun Sojin Najeriya Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa da Mutane a Zamfara
X whatsapp