Home Taska Kimanin Malamai 200 ne Suka bar Jami’ar KASU – ASUU

Kimanin Malamai 200 ne Suka bar Jami’ar KASU – ASUU

Kimanin Malamai 200 ne Suka bar Jami’ar KASU – ASUU

 

ƙungiyar malaman jami’o’i ta Najeriya (ASUU) reshen jami’ar jihar Kaduna (KASU) ta ce malaman jami’ar kimanin 200, ciki har da furofesoshi ne suka bar jami’ar sakamakon rashin kyawun yanayin aiki da kuma rashin aiwatar da yarjejeniyar da gwamnatin tarayya ta ƙulla da ASUU a 2025.

Shugaban ASUU-KASU, Dakta Abubakar Abdullahi, ya bayyana haka a wani taron manema labarai ranar Litinin, inda ya ce mafi yawan malaman da suka fice sun samu aiki a sabbin jami’o’i da ke ciki da wajen jihar Kaduna.

Ya ce rashin aiwatar da yarjejeniyar, wadda ta fara aiki tun watan Janairun 2026, ya sanya malaman KASU cikin mafi ƙarancin albashi tsakanin ma’aikatan jami’o’i a Najeriya.

ASUU ta bai wa gwamnatin jihar Kaduna da mahukuntan jami’ar wa’adin makonni biyu su fara aiwatar da yarjejeniyar, tare da gargaɗin cewa rashin yin hakan na iya jawo yajin aikin sai baba-ta-gani a jami’ar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Anambara: Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'addan IPOB/ESN, Sun Kwato MakamaiHukumar Kwastam ta Kano ta Mika Magungunan da ba a yi wa Rijista ba ga NAFDAC, ta Kuma yi Alƙawarin Tsaurara Matakan Aiki.Operation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Kawar da 'Yan Ta'adda 36 a BornoFamadewa, Ribadu da Shirin Tsaron Kwanaki 90: Yadda YAShuaib ya Binciki Sanarwar OnanugaLabarin NIPSS Ya Bayyana Cin Zarafin Babban Jami'in Sojan Ruwa, Rear Admiral AA MustaphaƊaliban PRNigeria Sun Yaba da Gyare-Gyaren FRSC, Sun Nemi Ƙarin Ƙarfafa Sadarwa Kan Tsaron HanyaYadda Dalibai 4 Almajirai Suka Mutu Bayan Cin Kife da Ake Zargi da Guba a KanoSojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Sace a Dajin KatsinaTinubu Ya Nada Abel Enitan A Matsayin Sabon Shugaban Ma'aikatan TarayyaRundunar Sojin Ruwan Najeriya ta Ceto Mutane 22 Daga Hannun Ƴan Fashin Teku Kimanin Malamai 200 ne Suka bar Jami'ar KASU - ASUUHukumar EFCC ta Gurfanar da Mutumin da ake Zargi da Damfarar Maniyyata Aikin HajjiKashi 40 Cikin 100 Kawai na Cibiyoyin Kiwon Lafiya a Duniya ke da Tsabta - MDDDakarun Sojin Najeriya Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa da Mutane a Zamfara
X whatsapp