Home Taska Rundunar Sojin Ruwan Najeriya ta Ceto Mutane 22 Daga Hannun Ƴan Fashin...

Rundunar Sojin Ruwan Najeriya ta Ceto Mutane 22 Daga Hannun Ƴan Fashin Teku 

Rundunar Sojin Ruwan Najeriya ta Ceto Mutane 22 Daga Hannun Ƴan Fashin Teku

 

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta ce ta ceto fasinjoji 22 da ƴan fashin teku suka yi garkuwa da su tare da ƙwato wani jirgin ruwa na fasinja da aka sace a hanyar ruwa tsakanin Calabar da Ibaka a jihar Akwa Ibom.

Rundunar ta bayyana cewa an gudanar da aikin ceton ne bayan samun rahoton harin da aka kai wa jirgin a ranar 11 ga watan Agusta.

A cewar daraktan yaɗa labaran rundunar, Kyaftin Abiodun Folorunsho, maharan sun tare jirgin ne jim kaɗan bayan ya wuce yankin Enwang, inda suka yi awon gaba da jirgin tare da sace fasinjojin da ke cikinsa.

Ya ce jami’an sansanin FOB Ibaka sun haɗa gwiwa da Operation Delta Safe da kuma ƴansandan ruwa domin gano waɗanda aka sace da kuma kwato jirgin.

Rundunar ta ce an kai waɗanda aka ceto asibitin FOB Ibaka domin yi musu gwajin lafiya da ba su agajin gaggawa kafin mayar da su Calabar tare da jirgin da aka ƙwato.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Ƴan Sandan Legas Sun Kama Mutum 4 da Ake Zargi da Fashin Daji, Sun Kwato Wayoyin Hannu 25, Kwamfutoci da Kayan Ado na ZinareRundunar Sojin Ruwa Ta Rusa Wuraren Tace Mai Ba bisa Ka’ida Ba, Ta Kwato Lita 350 na AGO a Rivers2027: Yahaya Bello Ya Tara Masu Daidaita Ayyuka na A4A a Arewa ta Tsakiya Domin sake Zaban TinubuSojoji Sun Kama Mutum 2 da ake Zargi da Taimakawa Ƴan Ta’adda, Sun Kwace Kayayyakin Babur a YobePDP Ta Yi Gargadi Kan Zargin Tattara Katunan Zabe PVC da Bayanan Asusun Banki a GombeRundunar Sojojin Najeriya ta Sauya Manyan Janarori Zuwa Muhimman Mukamai na Aiki da DabaruHukumar INEC za ta ƙaddamar da Na’urar Bibiyar shirye-shiryen Zaɓen 2027 kai TsayeDaliban Tallafin Horarwa na Prnigeria Sun Ziyarci Emirate FM, Sun Samu Kyawawan Bayani Kan Watsa Labarai na DijitalNSCIA ta yi Allah Wadai da Nuna Bambancin Addini a Ci gaba da Tsare El-RufaiSarkin Ilorin Ya Yaba da Tallafin Horarwa na PRNigeria Wajen Shirya Masu Watsa Labarai na Nan GabaNDLEA Ta Kama Mai Safarar Hodar Iblis da ake Zargi da Laifi Akan Jigilar Kaya a Saudiyya, ta Kuma Kama Kwayoyi Masu Yaduwa Sama Da Miliyan 2Gwamnatin Tarayya ta Yaba da N5.41 Trillion da Kwastam ta Tara, Ta Nemi a bi Ka'idojin Duniya Hukumar Kwastam Ta Naɗa DCG, ACG 5, ta yi Nazarin Yadda aka Samu Kuɗin Shiga2027: HURIWA Ta Bukaci Ƴan Sanda da su Gurfanar da Ƴan Siyasa Kan Zargin Kalamai Masu Tada HankaliSojoji Sun Tarwatsa Maboyar Ƴan Ta'adda, Sun Kwace Bindigogin AK-47 a Sokoto 
X whatsapp