Home Taska Rundunar Sojin Ruwan Najeriya ta Ceto Mutane 22 Daga Hannun Ƴan Fashin...

Rundunar Sojin Ruwan Najeriya ta Ceto Mutane 22 Daga Hannun Ƴan Fashin Teku 

Rundunar Sojin Ruwan Najeriya ta Ceto Mutane 22 Daga Hannun Ƴan Fashin Teku

 

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta ce ta ceto fasinjoji 22 da ƴan fashin teku suka yi garkuwa da su tare da ƙwato wani jirgin ruwa na fasinja da aka sace a hanyar ruwa tsakanin Calabar da Ibaka a jihar Akwa Ibom.

Rundunar ta bayyana cewa an gudanar da aikin ceton ne bayan samun rahoton harin da aka kai wa jirgin a ranar 11 ga watan Agusta.

A cewar daraktan yaɗa labaran rundunar, Kyaftin Abiodun Folorunsho, maharan sun tare jirgin ne jim kaɗan bayan ya wuce yankin Enwang, inda suka yi awon gaba da jirgin tare da sace fasinjojin da ke cikinsa.

Ya ce jami’an sansanin FOB Ibaka sun haɗa gwiwa da Operation Delta Safe da kuma ƴansandan ruwa domin gano waɗanda aka sace da kuma kwato jirgin.

Rundunar ta ce an kai waɗanda aka ceto asibitin FOB Ibaka domin yi musu gwajin lafiya da ba su agajin gaggawa kafin mayar da su Calabar tare da jirgin da aka ƙwato.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Anambara: Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'addan IPOB/ESN, Sun Kwato MakamaiHukumar Kwastam ta Kano ta Mika Magungunan da ba a yi wa Rijista ba ga NAFDAC, ta Kuma yi Alƙawarin Tsaurara Matakan Aiki.Operation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Kawar da 'Yan Ta'adda 36 a BornoFamadewa, Ribadu da Shirin Tsaron Kwanaki 90: Yadda YAShuaib ya Binciki Sanarwar OnanugaLabarin NIPSS Ya Bayyana Cin Zarafin Babban Jami'in Sojan Ruwa, Rear Admiral AA MustaphaƊaliban PRNigeria Sun Yaba da Gyare-Gyaren FRSC, Sun Nemi Ƙarin Ƙarfafa Sadarwa Kan Tsaron HanyaYadda Dalibai 4 Almajirai Suka Mutu Bayan Cin Kife da Ake Zargi da Guba a KanoSojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Sace a Dajin KatsinaTinubu Ya Nada Abel Enitan A Matsayin Sabon Shugaban Ma'aikatan TarayyaRundunar Sojin Ruwan Najeriya ta Ceto Mutane 22 Daga Hannun Ƴan Fashin Teku Kimanin Malamai 200 ne Suka bar Jami'ar KASU - ASUUHukumar EFCC ta Gurfanar da Mutumin da ake Zargi da Damfarar Maniyyata Aikin HajjiKashi 40 Cikin 100 Kawai na Cibiyoyin Kiwon Lafiya a Duniya ke da Tsabta - MDDDakarun Sojin Najeriya Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa da Mutane a Zamfara
X whatsapp