Home Taska Ƴan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je...

Ƴan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a Zamfara

'Yan Bindiga

Ƴan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a Zamfara

Ƴan bindigar da suka yi garkuwa da mutum kusan 40 bayan sun tafi yin sulhu da yanfashin daji a ƙaramar hukumar Maradun na Jihar Zamfara sun buƙaci a biya naira miliyan 100 kafin su sako su.

Mutanen da aka yi garukuwar da su a ranar Lahadi da yamma galibinsu dattawa ne, kamar yadda danmajalisar dokokin jiha mai wakiltar yankin na Maradun Maharazu Salisu ya shaida wa BBC.

Lamarin ya faru ne a ƙauyen Magamin Diddi wanda rahotanni suka ce yana a kusa da ɗaya daga cikin dazukan da ƴan fashin daji ke da sansani

A tattaunawarsa da BBC, Sunusi Ahmed Dosara ya ce: “Tun wata uku da suka wuce (ɓarayi) sun hana su (ƙauyen) zaman lafiya, ana cikin haka ne sai ɓarayin suka kwaɗaita musu cewa su zo a yi sulhu domin su bar su, su riƙa cin kasuwa.

“To daga nan sai dattijai suka je daji domin haɗuwa da ƴan bindiga, amma a lokacin da suka je sai ɓarayin suka riƙe su, sanan suka sako wasu daga cikinsu suka ce ba za su sake su ba sai an cika musu wasu sharuɗaɗa”.

Shugaban ƙaramar hukumar ya ce daga ƙididdigar da suka yi mutanen da ƴan fashin dajin suka riƙe “sun kai 39”.

Ya ƙara da cewa dukkanin mutanen da ake riƙe da su “maza ne dattawa”.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp