Ƴan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a Zamfara
Ƴan bindigar da suka yi garkuwa da mutum kusan 40 bayan sun tafi yin sulhu da yanfashin daji a ƙaramar hukumar Maradun na Jihar Zamfara sun buƙaci a biya naira miliyan 100 kafin su sako su.
Mutanen da aka yi garukuwar da su a ranar Lahadi da yamma galibinsu dattawa ne, kamar yadda danmajalisar dokokin jiha mai wakiltar yankin na Maradun Maharazu Salisu ya shaida wa BBC.
Lamarin ya faru ne a ƙauyen Magamin Diddi wanda rahotanni suka ce yana a kusa da ɗaya daga cikin dazukan da ƴan fashin daji ke da sansani
Read Also:
A tattaunawarsa da BBC, Sunusi Ahmed Dosara ya ce: “Tun wata uku da suka wuce (ɓarayi) sun hana su (ƙauyen) zaman lafiya, ana cikin haka ne sai ɓarayin suka kwaɗaita musu cewa su zo a yi sulhu domin su bar su, su riƙa cin kasuwa.
“To daga nan sai dattijai suka je daji domin haɗuwa da ƴan bindiga, amma a lokacin da suka je sai ɓarayin suka riƙe su, sanan suka sako wasu daga cikinsu suka ce ba za su sake su ba sai an cika musu wasu sharuɗaɗa”.
Shugaban ƙaramar hukumar ya ce daga ƙididdigar da suka yi mutanen da ƴan fashin dajin suka riƙe “sun kai 39”.
Ya ƙara da cewa dukkanin mutanen da ake riƙe da su “maza ne dattawa”.










