Home Taska Gwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba – Ministan...

Gwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba – Ministan Matasa

Gwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba – Ministan Matasa

 

Ministan Raya Matasa na Najeriya, Ayodele Olawande, ya bayyana cewa har yanzu gwamnatin tarayya ba ta amince da sauya kayan masu yi wa ƙasa hidima na NYSC zuwa kayan Kampala ba.

A wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X, ministan ya ce rahotannin da ke cewa an amince da amfani da Kampala a maimakon kaki sun fassara kalamansa ba daidai ba, bayan wata hira da ya yi da gidan talabijin na Channels.

Ya ce lokacin hirar ya ambaci Adire da Ankara ne kawai a matsayin wasu daga cikin shawarwarin da ake tattaunawa a kan su, yana mai jaddada cewa har yanzu ba a yanke hukunci kan irin kayan ko tsarin da za a yi amfani da shi ba.

Ya ce, “Manufata ita ce in bayar da misalai na wasu daga cikin shawarwarin da aka gabatar yayin tattaunawa. Ban sanar da cewa an amince da wani irin kaya ya maye gurbin kakin NYSC na yanzu ba.”

Ministan ya ce duk wata matsaya da za a cimma za ta kasance ne bayan tattaunawa da masu ruwa da tsaki tare da la’akari da abin da ya fi amfani ga shirin NYSC da kuma Najeriya baki ɗaya.

Mista Olawande ya ce “sauye-sauyen da ake shiryawa na da nufin inganta shirin ta hanyar ƙara wa matasa damar samun aikin yi, bunƙasa harkokin kasuwanci, ƙarfafa haɗin kan ƙasa, inganta ayyukan yi da kuma sauƙaƙa musu shiga rayuwar aiki bayan kammala karatu.”

Ya kuma ce “bai kamata muhawarar da ake yi kan kayan NYSC ta mamaye hankalin jama’a fiye da manyan sauye-sauyen da gwamnati ke shiryawa domin ƙarfafa matasan Najeriya da kuma bunƙasa ci gaban ƙasar.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp