Home Taska Gwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba – Ministan...

Gwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba – Ministan Matasa

Gwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba – Ministan Matasa

 

Ministan Raya Matasa na Najeriya, Ayodele Olawande, ya bayyana cewa har yanzu gwamnatin tarayya ba ta amince da sauya kayan masu yi wa ƙasa hidima na NYSC zuwa kayan Kampala ba.

A wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X, ministan ya ce rahotannin da ke cewa an amince da amfani da Kampala a maimakon kaki sun fassara kalamansa ba daidai ba, bayan wata hira da ya yi da gidan talabijin na Channels.

Ya ce lokacin hirar ya ambaci Adire da Ankara ne kawai a matsayin wasu daga cikin shawarwarin da ake tattaunawa a kan su, yana mai jaddada cewa har yanzu ba a yanke hukunci kan irin kayan ko tsarin da za a yi amfani da shi ba.

Ya ce, “Manufata ita ce in bayar da misalai na wasu daga cikin shawarwarin da aka gabatar yayin tattaunawa. Ban sanar da cewa an amince da wani irin kaya ya maye gurbin kakin NYSC na yanzu ba.”

Ministan ya ce duk wata matsaya da za a cimma za ta kasance ne bayan tattaunawa da masu ruwa da tsaki tare da la’akari da abin da ya fi amfani ga shirin NYSC da kuma Najeriya baki ɗaya.

Mista Olawande ya ce “sauye-sauyen da ake shiryawa na da nufin inganta shirin ta hanyar ƙara wa matasa damar samun aikin yi, bunƙasa harkokin kasuwanci, ƙarfafa haɗin kan ƙasa, inganta ayyukan yi da kuma sauƙaƙa musu shiga rayuwar aiki bayan kammala karatu.”

Ya kuma ce “bai kamata muhawarar da ake yi kan kayan NYSC ta mamaye hankalin jama’a fiye da manyan sauye-sauyen da gwamnati ke shiryawa domin ƙarfafa matasan Najeriya da kuma bunƙasa ci gaban ƙasar.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp