Home Taska Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar Tsaro

Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar Tsaro

Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar Tsaro

 

Gwamnonin yankin arewacin Najeriya sun kafa asusun tsaron yankin tare da rantsar da kwamitin amintattun waɗanda za su lura da asusun da jagorantar aiki da kuɗaɗen.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da gwamnan Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, kuma shugaban ƙungiyar gwamnonin yankin.

“A yau mun cimma wani muhimman mataki a ƙoƙarin bai-ɗaya da muke yi kan magance ƙalubalen da suka addabi Arewacin Najeriya, musamman matsalar rashin tsaro. A dukkan jihohin Arewa, barazanar ‘yan bindiga, ta’addanci, garkuwa da mutane domin neman kuɗin fansa shaye-shayen miyagun ƙwayoyi da sauran nau’o’in aikata laifuka na ci gaba da kawo cikas ga zaman lafiya.”

Ya ce sun cimma matsaya bayan tarukansu a Abuja da Kaduna cewa yankin na buƙatar wasu matakai na gaggawa, “Duk da cewa gwamnatin tarayya ce ke da alhakin tabbatar da tsaron ƙasa, akwai buƙatar jihohin arewa su ƙara bayar da gudunmawa domin tallafa wa ƙoƙarin hukumomin tsaro na tarayya wajen musayar bayanan sirri da sauransu.”

Ya ce saboda haka ne suka amince da kafa asusun tsaron arewacin Najeriya. “An ƙirƙiri wannan asusu ne domin tattara kuɗaɗe da ƙarfafa haɗin gwiwar tsaro da inganta musayar bayanan sirri da kuma taimaka wa gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro wajen sauke nauyin kare rayuka da dukiyoyin al’umma.”

Mambobin Kwamitin Amintattu da za a rantsar a yau gwamnamocin jihohin Arewa goma sha tara ne suka zaɓe su bisa cancanta. Dukkansu mutane ne da suka yi fice a fannoni daban-daban na hidima ga ƙasarmu. Muna da cikakken yaƙinin cewa za su kawo ƙwarewa, gaskiya, kishin ƙasa da fahimtar gaggawar wannan aiki.

Gwamna ya ce akwai buƙatar su ƙara ƙaimi wajen magance tushen matsalolin rashin tsaro a yankin da ya ce sun ƙunshi talauci da jahilci da rashin aikin yi da yawan yara da ba sa zuwa makaranta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Ƴan Sandan Legas Sun Kama Mutum 4 da Ake Zargi da Fashin Daji, Sun Kwato Wayoyin Hannu 25, Kwamfutoci da Kayan Ado na ZinareRundunar Sojin Ruwa Ta Rusa Wuraren Tace Mai Ba bisa Ka’ida Ba, Ta Kwato Lita 350 na AGO a Rivers2027: Yahaya Bello Ya Tara Masu Daidaita Ayyuka na A4A a Arewa ta Tsakiya Domin sake Zaban TinubuSojoji Sun Kama Mutum 2 da ake Zargi da Taimakawa Ƴan Ta’adda, Sun Kwace Kayayyakin Babur a YobePDP Ta Yi Gargadi Kan Zargin Tattara Katunan Zabe PVC da Bayanan Asusun Banki a GombeRundunar Sojojin Najeriya ta Sauya Manyan Janarori Zuwa Muhimman Mukamai na Aiki da DabaruHukumar INEC za ta ƙaddamar da Na’urar Bibiyar shirye-shiryen Zaɓen 2027 kai TsayeDaliban Tallafin Horarwa na Prnigeria Sun Ziyarci Emirate FM, Sun Samu Kyawawan Bayani Kan Watsa Labarai na DijitalNSCIA ta yi Allah Wadai da Nuna Bambancin Addini a Ci gaba da Tsare El-RufaiSarkin Ilorin Ya Yaba da Tallafin Horarwa na PRNigeria Wajen Shirya Masu Watsa Labarai na Nan GabaNDLEA Ta Kama Mai Safarar Hodar Iblis da ake Zargi da Laifi Akan Jigilar Kaya a Saudiyya, ta Kuma Kama Kwayoyi Masu Yaduwa Sama Da Miliyan 2Gwamnatin Tarayya ta Yaba da N5.41 Trillion da Kwastam ta Tara, Ta Nemi a bi Ka'idojin Duniya Hukumar Kwastam Ta Naɗa DCG, ACG 5, ta yi Nazarin Yadda aka Samu Kuɗin Shiga2027: HURIWA Ta Bukaci Ƴan Sanda da su Gurfanar da Ƴan Siyasa Kan Zargin Kalamai Masu Tada HankaliSojoji Sun Tarwatsa Maboyar Ƴan Ta'adda, Sun Kwace Bindigogin AK-47 a Sokoto 
X whatsapp