Home Taska Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar Tsaro

Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar Tsaro

Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar Tsaro

 

Gwamnonin yankin arewacin Najeriya sun kafa asusun tsaron yankin tare da rantsar da kwamitin amintattun waɗanda za su lura da asusun da jagorantar aiki da kuɗaɗen.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da gwamnan Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, kuma shugaban ƙungiyar gwamnonin yankin.

“A yau mun cimma wani muhimman mataki a ƙoƙarin bai-ɗaya da muke yi kan magance ƙalubalen da suka addabi Arewacin Najeriya, musamman matsalar rashin tsaro. A dukkan jihohin Arewa, barazanar ‘yan bindiga, ta’addanci, garkuwa da mutane domin neman kuɗin fansa shaye-shayen miyagun ƙwayoyi da sauran nau’o’in aikata laifuka na ci gaba da kawo cikas ga zaman lafiya.”

Ya ce sun cimma matsaya bayan tarukansu a Abuja da Kaduna cewa yankin na buƙatar wasu matakai na gaggawa, “Duk da cewa gwamnatin tarayya ce ke da alhakin tabbatar da tsaron ƙasa, akwai buƙatar jihohin arewa su ƙara bayar da gudunmawa domin tallafa wa ƙoƙarin hukumomin tsaro na tarayya wajen musayar bayanan sirri da sauransu.”

Ya ce saboda haka ne suka amince da kafa asusun tsaron arewacin Najeriya. “An ƙirƙiri wannan asusu ne domin tattara kuɗaɗe da ƙarfafa haɗin gwiwar tsaro da inganta musayar bayanan sirri da kuma taimaka wa gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro wajen sauke nauyin kare rayuka da dukiyoyin al’umma.”

Mambobin Kwamitin Amintattu da za a rantsar a yau gwamnamocin jihohin Arewa goma sha tara ne suka zaɓe su bisa cancanta. Dukkansu mutane ne da suka yi fice a fannoni daban-daban na hidima ga ƙasarmu. Muna da cikakken yaƙinin cewa za su kawo ƙwarewa, gaskiya, kishin ƙasa da fahimtar gaggawar wannan aiki.

Gwamna ya ce akwai buƙatar su ƙara ƙaimi wajen magance tushen matsalolin rashin tsaro a yankin da ya ce sun ƙunshi talauci da jahilci da rashin aikin yi da yawan yara da ba sa zuwa makaranta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Anambara: Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'addan IPOB/ESN, Sun Kwato MakamaiHukumar Kwastam ta Kano ta Mika Magungunan da ba a yi wa Rijista ba ga NAFDAC, ta Kuma yi Alƙawarin Tsaurara Matakan Aiki.Operation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Kawar da 'Yan Ta'adda 36 a BornoFamadewa, Ribadu da Shirin Tsaron Kwanaki 90: Yadda YAShuaib ya Binciki Sanarwar OnanugaLabarin NIPSS Ya Bayyana Cin Zarafin Babban Jami'in Sojan Ruwa, Rear Admiral AA MustaphaƊaliban PRNigeria Sun Yaba da Gyare-Gyaren FRSC, Sun Nemi Ƙarin Ƙarfafa Sadarwa Kan Tsaron HanyaYadda Dalibai 4 Almajirai Suka Mutu Bayan Cin Kife da Ake Zargi da Guba a KanoSojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Sace a Dajin KatsinaTinubu Ya Nada Abel Enitan A Matsayin Sabon Shugaban Ma'aikatan TarayyaRundunar Sojin Ruwan Najeriya ta Ceto Mutane 22 Daga Hannun Ƴan Fashin Teku Kimanin Malamai 200 ne Suka bar Jami'ar KASU - ASUUHukumar EFCC ta Gurfanar da Mutumin da ake Zargi da Damfarar Maniyyata Aikin HajjiKashi 40 Cikin 100 Kawai na Cibiyoyin Kiwon Lafiya a Duniya ke da Tsabta - MDDDakarun Sojin Najeriya Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa da Mutane a Zamfara
X whatsapp