Home Taska ɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr...

ɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi 

ɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi 

 

Ƙungiyar Amnesty International ta yi Allah-wadai da kamawa da tsare Dr Bashir Kurfi, lamarin da ya biyo bayan jawabin da ya game da matsalolin tsaro.

A wata tattaunawa da ya yi da tashar talabijin Trust, Dr Kurfi ya zargi gwamnatin jihar Katsinda da hannu a ɗaukar nauyin ƴanbindiga zuwa Hajji.

A ranar Laraba ne aka gabatar da malamin jami’ar a kotun Majistare a Katsina bayan rundunar ƴansandan jihar ta tuhume shi ƙazafi da ɓata suna.

Alƙalin kotun mai shari’a Zaharaddeen Kofar Soro ne ya buƙaci ƴansanda su cigaba da tsare wanda ake ƙara har zuwa lokacin da za a cigaba da sauraron shari’ar.

Da take jawabi kan batun, Amnesty ta ce Kurfi ya amsa gayyatar ƴansanda ne a ranar Talata 7 ga watan Yuliln 2026 domin amsa tambayoyi, amma a cewar ƙungiyar sai aka faɗa masa cewa za a tsare.

“Yanzu ana ƙoƙarin ganin an tsare shi na tsawon lokaci ta hanyar ƙirƙirar tuhume-tuhume,” in ji ƙungiyar, wanda a cewarta karya ƴancin tofa albarkacin baki ne.

“Gwamnatin jihar Katsina na so ne ta hukunta kawai don ya yi tambayoyi game da yadda take kula da harkokin da suka shafi yaƙi da ƴanbindiga maimakon ta bincika abin da ya faɗa.”

Amnesty ta ce an tsare Kurfi ne domin a tsoratar da mutane su daina tsokaci kan gwamnati. “Bai kamata a hukunta mutum ba domin ya soki gwamnti. Dr Kurfi bai aikata laifin komai ba, kuma tsare shi cin amanar aiki ne domin yana da ƴancin tambaya ko sukar yadda gwamnati take gudanar da aiki.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Ƴan Sandan Legas Sun Kama Mutum 4 da Ake Zargi da Fashin Daji, Sun Kwato Wayoyin Hannu 25, Kwamfutoci da Kayan Ado na ZinareRundunar Sojin Ruwa Ta Rusa Wuraren Tace Mai Ba bisa Ka’ida Ba, Ta Kwato Lita 350 na AGO a Rivers2027: Yahaya Bello Ya Tara Masu Daidaita Ayyuka na A4A a Arewa ta Tsakiya Domin sake Zaban TinubuSojoji Sun Kama Mutum 2 da ake Zargi da Taimakawa Ƴan Ta’adda, Sun Kwace Kayayyakin Babur a YobePDP Ta Yi Gargadi Kan Zargin Tattara Katunan Zabe PVC da Bayanan Asusun Banki a GombeRundunar Sojojin Najeriya ta Sauya Manyan Janarori Zuwa Muhimman Mukamai na Aiki da DabaruHukumar INEC za ta ƙaddamar da Na’urar Bibiyar shirye-shiryen Zaɓen 2027 kai TsayeDaliban Tallafin Horarwa na Prnigeria Sun Ziyarci Emirate FM, Sun Samu Kyawawan Bayani Kan Watsa Labarai na DijitalNSCIA ta yi Allah Wadai da Nuna Bambancin Addini a Ci gaba da Tsare El-RufaiSarkin Ilorin Ya Yaba da Tallafin Horarwa na PRNigeria Wajen Shirya Masu Watsa Labarai na Nan GabaNDLEA Ta Kama Mai Safarar Hodar Iblis da ake Zargi da Laifi Akan Jigilar Kaya a Saudiyya, ta Kuma Kama Kwayoyi Masu Yaduwa Sama Da Miliyan 2Gwamnatin Tarayya ta Yaba da N5.41 Trillion da Kwastam ta Tara, Ta Nemi a bi Ka'idojin Duniya Hukumar Kwastam Ta Naɗa DCG, ACG 5, ta yi Nazarin Yadda aka Samu Kuɗin Shiga2027: HURIWA Ta Bukaci Ƴan Sanda da su Gurfanar da Ƴan Siyasa Kan Zargin Kalamai Masu Tada HankaliSojoji Sun Tarwatsa Maboyar Ƴan Ta'adda, Sun Kwace Bindigogin AK-47 a Sokoto 
X whatsapp