Home Taska ɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr...

ɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi 

ɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi 

 

Ƙungiyar Amnesty International ta yi Allah-wadai da kamawa da tsare Dr Bashir Kurfi, lamarin da ya biyo bayan jawabin da ya game da matsalolin tsaro.

A wata tattaunawa da ya yi da tashar talabijin Trust, Dr Kurfi ya zargi gwamnatin jihar Katsinda da hannu a ɗaukar nauyin ƴanbindiga zuwa Hajji.

A ranar Laraba ne aka gabatar da malamin jami’ar a kotun Majistare a Katsina bayan rundunar ƴansandan jihar ta tuhume shi ƙazafi da ɓata suna.

Alƙalin kotun mai shari’a Zaharaddeen Kofar Soro ne ya buƙaci ƴansanda su cigaba da tsare wanda ake ƙara har zuwa lokacin da za a cigaba da sauraron shari’ar.

Da take jawabi kan batun, Amnesty ta ce Kurfi ya amsa gayyatar ƴansanda ne a ranar Talata 7 ga watan Yuliln 2026 domin amsa tambayoyi, amma a cewar ƙungiyar sai aka faɗa masa cewa za a tsare.

“Yanzu ana ƙoƙarin ganin an tsare shi na tsawon lokaci ta hanyar ƙirƙirar tuhume-tuhume,” in ji ƙungiyar, wanda a cewarta karya ƴancin tofa albarkacin baki ne.

“Gwamnatin jihar Katsina na so ne ta hukunta kawai don ya yi tambayoyi game da yadda take kula da harkokin da suka shafi yaƙi da ƴanbindiga maimakon ta bincika abin da ya faɗa.”

Amnesty ta ce an tsare Kurfi ne domin a tsoratar da mutane su daina tsokaci kan gwamnati. “Bai kamata a hukunta mutum ba domin ya soki gwamnti. Dr Kurfi bai aikata laifin komai ba, kuma tsare shi cin amanar aiki ne domin yana da ƴancin tambaya ko sukar yadda gwamnati take gudanar da aiki.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga PantamiGazawar Demarketing: Yadda Sukar Rarara Mai Cike da Kiyayya ga Pantami Ya Rushe Daga Yushau A. ShuaibƘungiyar NARD ta yi Barazanar Shiga Yajin AikiDakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Ƴan Bindiga 3 Sun Ceto Mutane 9 da akai Garkuwa da suƳan Bindiga sun kai Hari a Kotun Shari'a da ke Jihar KatsinaBa ma Goyon Bayan a Riƙa Tura Sojoji Domin Aikin Tsaro a Lokacin Zaɓe - INECJam'iyyar NDC ta Buƙaci Sanata Hanga da Gaya da su Sake Tunani Kan Sauya SheƙaYan Bindiga Sun Kashe Kanal Abdussalam Ude Sun Raunata MatarsaMutane 15 Sun Mutu a Sabon Harin Yan Bindiga a Jihar Benue Zaɓen 2027: Uba Sani ya zaɓi MataimakinsaJami'an Tsaro Sun Kuɓutar da Mutane 32 Yayin da 4 Suka Mutu a Jihar Sokoto 
X whatsapp