Home Taska ɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr...

ɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi 

ɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi 

 

Ƙungiyar Amnesty International ta yi Allah-wadai da kamawa da tsare Dr Bashir Kurfi, lamarin da ya biyo bayan jawabin da ya game da matsalolin tsaro.

A wata tattaunawa da ya yi da tashar talabijin Trust, Dr Kurfi ya zargi gwamnatin jihar Katsinda da hannu a ɗaukar nauyin ƴanbindiga zuwa Hajji.

A ranar Laraba ne aka gabatar da malamin jami’ar a kotun Majistare a Katsina bayan rundunar ƴansandan jihar ta tuhume shi ƙazafi da ɓata suna.

Alƙalin kotun mai shari’a Zaharaddeen Kofar Soro ne ya buƙaci ƴansanda su cigaba da tsare wanda ake ƙara har zuwa lokacin da za a cigaba da sauraron shari’ar.

Da take jawabi kan batun, Amnesty ta ce Kurfi ya amsa gayyatar ƴansanda ne a ranar Talata 7 ga watan Yuliln 2026 domin amsa tambayoyi, amma a cewar ƙungiyar sai aka faɗa masa cewa za a tsare.

“Yanzu ana ƙoƙarin ganin an tsare shi na tsawon lokaci ta hanyar ƙirƙirar tuhume-tuhume,” in ji ƙungiyar, wanda a cewarta karya ƴancin tofa albarkacin baki ne.

“Gwamnatin jihar Katsina na so ne ta hukunta kawai don ya yi tambayoyi game da yadda take kula da harkokin da suka shafi yaƙi da ƴanbindiga maimakon ta bincika abin da ya faɗa.”

Amnesty ta ce an tsare Kurfi ne domin a tsoratar da mutane su daina tsokaci kan gwamnati. “Bai kamata a hukunta mutum ba domin ya soki gwamnti. Dr Kurfi bai aikata laifin komai ba, kuma tsare shi cin amanar aiki ne domin yana da ƴancin tambaya ko sukar yadda gwamnati take gudanar da aiki.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Anambara: Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'addan IPOB/ESN, Sun Kwato MakamaiHukumar Kwastam ta Kano ta Mika Magungunan da ba a yi wa Rijista ba ga NAFDAC, ta Kuma yi Alƙawarin Tsaurara Matakan Aiki.Operation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Kawar da 'Yan Ta'adda 36 a BornoFamadewa, Ribadu da Shirin Tsaron Kwanaki 90: Yadda YAShuaib ya Binciki Sanarwar OnanugaLabarin NIPSS Ya Bayyana Cin Zarafin Babban Jami'in Sojan Ruwa, Rear Admiral AA MustaphaƊaliban PRNigeria Sun Yaba da Gyare-Gyaren FRSC, Sun Nemi Ƙarin Ƙarfafa Sadarwa Kan Tsaron HanyaYadda Dalibai 4 Almajirai Suka Mutu Bayan Cin Kife da Ake Zargi da Guba a KanoSojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Sace a Dajin KatsinaTinubu Ya Nada Abel Enitan A Matsayin Sabon Shugaban Ma'aikatan TarayyaRundunar Sojin Ruwan Najeriya ta Ceto Mutane 22 Daga Hannun Ƴan Fashin Teku Kimanin Malamai 200 ne Suka bar Jami'ar KASU - ASUUHukumar EFCC ta Gurfanar da Mutumin da ake Zargi da Damfarar Maniyyata Aikin HajjiKashi 40 Cikin 100 Kawai na Cibiyoyin Kiwon Lafiya a Duniya ke da Tsabta - MDDDakarun Sojin Najeriya Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa da Mutane a Zamfara
X whatsapp