Home Taska Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar Benue

Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar Benue

'Yan Ta'adda

Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar Benue

 

Aƙalla mutum 10 aka kashe da sanyin safiyar Laraba bayan wasu mahara ɗauke da makamai sun kai hari ƙauyen Saai da ke gundumar Mbajir a ƙaramar hukumar Katsina-Ala ta jihar Benue.

Mazauna yankin sun ce maharan sun kutsa cikin ƙauyen da tsakar dare, inda suka riƙa harbe-harbe ba tare da ƙaƙƙautawa ba.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito wani mazaunin yankin na cewa wasu daga cikin mutanen sun jikkata sakamakon harbin bindiga, yayin da aka kashe wasu ciki har da Mchiaga Akaa Agbondo, wanda ya ce “an sassara shi da adda har ba a gane fuskarsa”.

Ya ƙara da cewa ana ci gaba da kula da wasu da suka jikkata a asibiti.

Shugaban ƙaramar hukumar Katsina-Ala, Justine Shaku, ya tabbatar da faruwar harin, amma ya ce har yanzu ba a tantance adadin mutanen da suka mutu ba, amma ya je yankin domin duba halin da ake ciki.

Gwamnan jihar Benue, Hyacinth Alia, ya yi Allah wadai da harin, inda ya yi zargin cewa maharan ƴan ta’adda ne da ke fakewa da sunan makiyaya, domi kawo cikas ga ayyukan noma da samar da abinci a jihar.

Gwamnan ya umarci jami’an tsaro su tura ƙarin dakaru zuwa yankin Saai da sauran ƙauyukan da ke makwabtaka da yankin domin farautar waɗanda suka kai harin, tare da ƙara tsaurara matakan tsaro ga manoma.

Rundunar ƴansanda ba ta fitar da wata saarwa game da harin ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp