Home Taska NMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba 

NMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba 

NMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man Kan Sayar da Farashin Fetur

 

Hukumar Kula da Harkokin ta Najeriya (NMDPRA) ta yi gargaɗin cewa za ta hukunta gidajen man da ke sayar da man fetur a farashin da bai yi daidai da farashin ɗanyen mai a kasuwar duniya ba.

A cikin wata sanarwa da kakakin hukumar, George Ene-Ita, ya fitar a ranar Laraba, ya ce hukumar na sane da raguwar farashin ɗanyen mai a duniya, inda ya ce dole ne farashin man fetur ya zo daidai da yadda farashin yake, kamar yadda dokar albarkatun mai ta 2021 a ƙasar ta tanada.

Ya ce hukumar ta riga ta gargaɗi kamfanonin kasuwancin mai da su guji ƙara farashi domin cin ribar da ta wuce ƙa’ida.

NMDPRA ta ce ana sa ido kan gidajen mai, kuma za a ɗauki matakin a kan duk wanda aka samu da laifi.

Wannan gargaɗi na zuwa ne bayan kiran da ƙaramin ministan albarkatun man fetur, Sanata Heineken Lokpobiri, ya yi ga hukumomin da su ɗauki mataki kan dillalan man.

Ya ce bayan dakatar da yaƙi tsakanin Iran da Amurka, ƴan Najeriya na sa ran ganin an rage farashin man fetur a ƙasar.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man Kan Sayar da Farashin FeturNECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin Najeriya
X whatsapp