Home SIYASA An faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi...

An faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi – Shettima

Shettima

An faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi – Shettima

 

Mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima ya bayyana yadda ya ce wasu suka yi ƙoƙarin haɗa shi da shugaban ƙasa Bola Tinubu, wata uku bayan fara mulkinsu.

Yayin da yake jawabi a wani taron ƙaddamar da littafin tarihin rayuwar tsohon shugaban ƙasar, Janar Yakubu Gowon a Abuja, babban birnin ƙasar, Shettima ya ce wasu mutane da bai ambaci sunayensu ba, waɗanda ya ce daga jiharsa ta Borno suke sun faɗa Shugaba Tinubu cewa Shettiman na kitsa kashe shi domin karɓar mulki.

“Bayan wata uku da kama mulkinmu, wasu mutane suka faɗa wa Tinubu cewa ina kitsa yadda zan kashe shi domin na karɓi mulkin ƙasar. Daga nan sai ya kirani ya ce zauna mutanenka sun zo sun faɗa min cewa na daina saka tufafin da Shettima ya bani.”

“Sai dai da kansa Shugaba Tinubun ya ce min bai yarda da labarin nasu ba, saboda lokacin da ka bani tufafin ina matsayin ɗantakara ne, ban ma ci zaɓen fitar da gwani ba, ballanta ka zama mataimakin shugaban ƙasa”, in ji shi.

Ya ce wasu mutanen sun faɗa wa Tinubun cewa ina shirin amfani da tufafiun domin kashe shi.

”Kuma Shugaban ya saka tufafin bayan hakan saboda bai yi imani da hakan ba.”

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp