Home SIYASA An faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi...

An faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi – Shettima

Shettima

An faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi – Shettima

 

Mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima ya bayyana yadda ya ce wasu suka yi ƙoƙarin haɗa shi da shugaban ƙasa Bola Tinubu, wata uku bayan fara mulkinsu.

Yayin da yake jawabi a wani taron ƙaddamar da littafin tarihin rayuwar tsohon shugaban ƙasar, Janar Yakubu Gowon a Abuja, babban birnin ƙasar, Shettima ya ce wasu mutane da bai ambaci sunayensu ba, waɗanda ya ce daga jiharsa ta Borno suke sun faɗa Shugaba Tinubu cewa Shettiman na kitsa kashe shi domin karɓar mulki.

“Bayan wata uku da kama mulkinmu, wasu mutane suka faɗa wa Tinubu cewa ina kitsa yadda zan kashe shi domin na karɓi mulkin ƙasar. Daga nan sai ya kirani ya ce zauna mutanenka sun zo sun faɗa min cewa na daina saka tufafin da Shettima ya bani.”

“Sai dai da kansa Shugaba Tinubun ya ce min bai yarda da labarin nasu ba, saboda lokacin da ka bani tufafin ina matsayin ɗantakara ne, ban ma ci zaɓen fitar da gwani ba, ballanta ka zama mataimakin shugaban ƙasa”, in ji shi.

Ya ce wasu mutanen sun faɗa wa Tinubun cewa ina shirin amfani da tufafiun domin kashe shi.

”Kuma Shugaban ya saka tufafin bayan hakan saboda bai yi imani da hakan ba.”

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp