Home SIYASA An faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi...

An faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi – Shettima

Shettima

An faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi – Shettima

 

Mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima ya bayyana yadda ya ce wasu suka yi ƙoƙarin haɗa shi da shugaban ƙasa Bola Tinubu, wata uku bayan fara mulkinsu.

Yayin da yake jawabi a wani taron ƙaddamar da littafin tarihin rayuwar tsohon shugaban ƙasar, Janar Yakubu Gowon a Abuja, babban birnin ƙasar, Shettima ya ce wasu mutane da bai ambaci sunayensu ba, waɗanda ya ce daga jiharsa ta Borno suke sun faɗa Shugaba Tinubu cewa Shettiman na kitsa kashe shi domin karɓar mulki.

“Bayan wata uku da kama mulkinmu, wasu mutane suka faɗa wa Tinubu cewa ina kitsa yadda zan kashe shi domin na karɓi mulkin ƙasar. Daga nan sai ya kirani ya ce zauna mutanenka sun zo sun faɗa min cewa na daina saka tufafin da Shettima ya bani.”

“Sai dai da kansa Shugaba Tinubun ya ce min bai yarda da labarin nasu ba, saboda lokacin da ka bani tufafin ina matsayin ɗantakara ne, ban ma ci zaɓen fitar da gwani ba, ballanta ka zama mataimakin shugaban ƙasa”, in ji shi.

Ya ce wasu mutanen sun faɗa wa Tinubun cewa ina shirin amfani da tufafiun domin kashe shi.

”Kuma Shugaban ya saka tufafin bayan hakan saboda bai yi imani da hakan ba.”

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp