Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar Mutane
Rundunar ƴansandan Najeriya ta ce ta tarwatsa wata ƙungiyar masu safarar mutane da ke gudanar da ayyukanta a Abuja, babban birnin ƙasar da wasu yankuna maƙwabta.
Hakan ya sa ƴansanda suka kuɓutar da mutum 30 ƴan asalin Mali da ake zargin an tsare su a jihar Nassarawa.
Read Also:
A cewar wata sanarwa da kakakin rundunar, Anthony Placid ya fitar, jami’an sun bankaɗo wasu ayyukan ƙungiyar a wani gida da ke Mararraba da Karu inda ake zargin an killace su.
Ƴansanda sun ce an kama mutum 13 da ake zargi suna da hannu a ƙungiyar.
A cewar ƴansanda, an soma bincike ne bayan da aka samu bayanan sirri kan ɓacewar baƙi da dama a Najeriya.
Placid ya ƙara da cewa binciken farko ya nuna cewa ƙungiyar tana yaudarar matasa daga ƙasashe irinsu Mali da Gabon inda suke yi musu alƙawarin ayyukan yi a Najeriya da kuma damar tsallakawa zuwa Turai.










