Home Taska Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu...

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar Mutane

DCP Anthony Okon Placid

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar Mutane

 

Rundunar ƴansandan Najeriya ta ce ta tarwatsa wata ƙungiyar masu safarar mutane da ke gudanar da ayyukanta a Abuja, babban birnin ƙasar da wasu yankuna maƙwabta.

Hakan ya sa ƴansanda suka kuɓutar da mutum 30 ƴan asalin Mali da ake zargin an tsare su a jihar Nassarawa.

A cewar wata sanarwa da kakakin rundunar, Anthony Placid ya fitar, jami’an sun bankaɗo wasu ayyukan ƙungiyar a wani gida da ke Mararraba da Karu inda ake zargin an killace su.

Ƴansanda sun ce an kama mutum 13 da ake zargi suna da hannu a ƙungiyar.

A cewar ƴansanda, an soma bincike ne bayan da aka samu bayanan sirri kan ɓacewar baƙi da dama a Najeriya.

Placid ya ƙara da cewa binciken farko ya nuna cewa ƙungiyar tana yaudarar matasa daga ƙasashe irinsu Mali da Gabon inda suke yi musu alƙawarin ayyukan yi a Najeriya da kuma damar tsallakawa zuwa Turai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp