Home Taska Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu...

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar Mutane

DCP Anthony Okon Placid

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar Mutane

 

Rundunar ƴansandan Najeriya ta ce ta tarwatsa wata ƙungiyar masu safarar mutane da ke gudanar da ayyukanta a Abuja, babban birnin ƙasar da wasu yankuna maƙwabta.

Hakan ya sa ƴansanda suka kuɓutar da mutum 30 ƴan asalin Mali da ake zargin an tsare su a jihar Nassarawa.

A cewar wata sanarwa da kakakin rundunar, Anthony Placid ya fitar, jami’an sun bankaɗo wasu ayyukan ƙungiyar a wani gida da ke Mararraba da Karu inda ake zargin an killace su.

Ƴansanda sun ce an kama mutum 13 da ake zargi suna da hannu a ƙungiyar.

A cewar ƴansanda, an soma bincike ne bayan da aka samu bayanan sirri kan ɓacewar baƙi da dama a Najeriya.

Placid ya ƙara da cewa binciken farko ya nuna cewa ƙungiyar tana yaudarar matasa daga ƙasashe irinsu Mali da Gabon inda suke yi musu alƙawarin ayyukan yi a Najeriya da kuma damar tsallakawa zuwa Turai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp