Mun Kashe Mayaƙan ISIS 175 – Rundunar Sojin Najeriya
Rundunar sojin Najeriya ta ce bayanan da ta samu bayan hare-hare da ta ƙaddamar tare da haɗin gwiwar sojojin Amurka a ƙarshen mako ya kashe mayaƙan ƙungiyar ISIS 175.
Sai dai babu wata kafa mai zaman kanta da ta tabbatar da wannan adadi ko kuma bayanan waɗanda aka kashen.
Read Also:
A ranar Juma’a ne shugabannin ƙasashen Amurka da Najeriya suka bayyana kashe wani kwamandan IS, mai suna Abu-Bilal al-Minuki da wasu mayaƙansa a wani hari ta sama da sojojin ƙasashen biyu suka kai gidansa a tafkin Chadi.
A farkon wannan wata ne sojojin Najeriya suka musanta rahotonnin kisan fararen hula a wasu hare-hare daban-daban a yankunan arewa maso gabasa da arewa maso yammacin ƙasar.
Tuni dai Majalisar Dinkin Duniya ta yi kiran gudanar da bincike game da batun











