Home SIYASA Farfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar Gombe

Farfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar Gombe

Isa Pantami

Farfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar Gombe

Tsohon ministan sadarwa na Najeriya, Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami, ya janye daga zaɓen fitar da gwani na gwamnan Gombe na jam’iyyar APC.

Cikin wani saƙo da Farfesa ya wallafa a shafukansa na sada zumunta ya ce ya ɗauki matakin ne bayan zargin jam’iyyar da karya dokar zaɓe da kuma rashin bin ƙa’idojin gudanar da zaɓen.

Farfesa Pantami ya ce ya fice daga zaɓen fitar da gwanin da ake sa ran gudanarwa ranar 21 ga Mayu “cikin nuna rashin amincewa da tsarin da aka yi”.

Ya ci gaba da cewa shugabannin jam’iyyar sun kasa yin bayani a kan yadda aka tsara zaɓen cikin aminci.

Ya ce an yi watsi da buƙatun da ya gabatar domin neman bayanai kan yadda za a tantance wakilai, da tsarin kaɗa ƙuri’a da wuraren tattara sakamako.

Pantami ya bayyana cewa ya ɗauki matakin ne bayan tuntuɓa da magoya baya da masu ruwa da tsaki, sakamakon abin da ya kira rashin gaskiya da kura-kurai a zaɓen fitar a gwani na ‘yan takarar majalisar dokoki da APC ta gudanar a jihar kwanan nan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp