Home SIYASA Farfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar Gombe

Farfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar Gombe

Isa Pantami

Farfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar Gombe

Tsohon ministan sadarwa na Najeriya, Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami, ya janye daga zaɓen fitar da gwani na gwamnan Gombe na jam’iyyar APC.

Cikin wani saƙo da Farfesa ya wallafa a shafukansa na sada zumunta ya ce ya ɗauki matakin ne bayan zargin jam’iyyar da karya dokar zaɓe da kuma rashin bin ƙa’idojin gudanar da zaɓen.

Farfesa Pantami ya ce ya fice daga zaɓen fitar da gwanin da ake sa ran gudanarwa ranar 21 ga Mayu “cikin nuna rashin amincewa da tsarin da aka yi”.

Ya ci gaba da cewa shugabannin jam’iyyar sun kasa yin bayani a kan yadda aka tsara zaɓen cikin aminci.

Ya ce an yi watsi da buƙatun da ya gabatar domin neman bayanai kan yadda za a tantance wakilai, da tsarin kaɗa ƙuri’a da wuraren tattara sakamako.

Pantami ya bayyana cewa ya ɗauki matakin ne bayan tuntuɓa da magoya baya da masu ruwa da tsaki, sakamakon abin da ya kira rashin gaskiya da kura-kurai a zaɓen fitar a gwani na ‘yan takarar majalisar dokoki da APC ta gudanar a jihar kwanan nan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp