Home Labarai Rundunar ‘Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami’anta 17 a Yobe

Rundunar ‘Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami’anta 17 a Yobe

DCP Anthony Okon Placid

Rundunar ‘Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami’anta 17 a Yobe

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tabbatar da kashe jami’anta 17 a wani harin da ’yan ta’adda suka kai wa wani sansanin horar da dakarun soji na musamman da ke Jihar Yobe.

Wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, DCP Anthony Okon Placid, ya fitar ranar Asabar ta ce an kashe jami’an ne ranar 8 ga watan Mayu.

“Rundunar ‘yan sandan Najeriya tana baƙin cikin sanar da kashe jami’anta 17 yayin da suke aikin bauta wa ƙasa sakamakon harin ta’addanci a Makarantar Dakarun Soji na Musamman da ke Buni Yadi a Ƙaramar Hukumar Gujba ta Jihar Yobe da sanyin safiyar 8 ga Mayun 2026,” in ji sanarwar.

Ta ƙara da cewa ‘yan sandan, waɗanda suke je makarantar domin samun horo na musamman, sun rasa rayukansu ne lokacin da ‘yan ta’adda suka kai jerin hare-hare a makarantar.

Sanarwar ta ce: “Kazalika jajirtattun dakarun sojin Najeriya da dama sun rasa rayukan a yayin da suke daƙile harin.”

Babban Sufeton ‘yansandan Nijeriya Olatunji Disu ya bayyana ‘yan sandan da aka kashe a matsayin waɗanda suke da “ƙarfin gwiwa da sadaukarwa” da nuna kishin ƙasa a yayin da suka halarci horo kan yaƙi da ta’addanci da wanzar da tsaro.

Ya miƙa saƙon ta’aziyyar ɗaukacin rundunar ‘yansandan Nijeriya ga iyalan jami’an da aka kashe tare da tabbatar musu cewa “ba za a taɓa mantawa da sadaukarwarsu ba.”

A wannan harin ta’addanci, jami’an tsaron Najeriya sun samu nasarar kashe mahara 50.

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, an kashe mayaƙa masu iƙirarin jihadi a lokacin da sojoji suka daƙile wani harin da ƙungiyar ISWAP ta kai a hedikwatar runduna ta 27 a garin Buni Gari da kuma wurin binciken ababen hawa na garin, wanda ke Jihar Yobe.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp