Home Labarai Rundunar ‘Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami’anta 17 a Yobe

Rundunar ‘Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami’anta 17 a Yobe

DCP Anthony Okon Placid

Rundunar ‘Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami’anta 17 a Yobe

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tabbatar da kashe jami’anta 17 a wani harin da ’yan ta’adda suka kai wa wani sansanin horar da dakarun soji na musamman da ke Jihar Yobe.

Wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, DCP Anthony Okon Placid, ya fitar ranar Asabar ta ce an kashe jami’an ne ranar 8 ga watan Mayu.

“Rundunar ‘yan sandan Najeriya tana baƙin cikin sanar da kashe jami’anta 17 yayin da suke aikin bauta wa ƙasa sakamakon harin ta’addanci a Makarantar Dakarun Soji na Musamman da ke Buni Yadi a Ƙaramar Hukumar Gujba ta Jihar Yobe da sanyin safiyar 8 ga Mayun 2026,” in ji sanarwar.

Ta ƙara da cewa ‘yan sandan, waɗanda suke je makarantar domin samun horo na musamman, sun rasa rayukansu ne lokacin da ‘yan ta’adda suka kai jerin hare-hare a makarantar.

Sanarwar ta ce: “Kazalika jajirtattun dakarun sojin Najeriya da dama sun rasa rayukan a yayin da suke daƙile harin.”

Babban Sufeton ‘yansandan Nijeriya Olatunji Disu ya bayyana ‘yan sandan da aka kashe a matsayin waɗanda suke da “ƙarfin gwiwa da sadaukarwa” da nuna kishin ƙasa a yayin da suka halarci horo kan yaƙi da ta’addanci da wanzar da tsaro.

Ya miƙa saƙon ta’aziyyar ɗaukacin rundunar ‘yansandan Nijeriya ga iyalan jami’an da aka kashe tare da tabbatar musu cewa “ba za a taɓa mantawa da sadaukarwarsu ba.”

A wannan harin ta’addanci, jami’an tsaron Najeriya sun samu nasarar kashe mahara 50.

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, an kashe mayaƙa masu iƙirarin jihadi a lokacin da sojoji suka daƙile wani harin da ƙungiyar ISWAP ta kai a hedikwatar runduna ta 27 a garin Buni Gari da kuma wurin binciken ababen hawa na garin, wanda ke Jihar Yobe.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp