Home Labarai Rundunar ‘Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami’anta 17 a Yobe

Rundunar ‘Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami’anta 17 a Yobe

DCP Anthony Okon Placid

Rundunar ‘Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami’anta 17 a Yobe

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tabbatar da kashe jami’anta 17 a wani harin da ’yan ta’adda suka kai wa wani sansanin horar da dakarun soji na musamman da ke Jihar Yobe.

Wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, DCP Anthony Okon Placid, ya fitar ranar Asabar ta ce an kashe jami’an ne ranar 8 ga watan Mayu.

“Rundunar ‘yan sandan Najeriya tana baƙin cikin sanar da kashe jami’anta 17 yayin da suke aikin bauta wa ƙasa sakamakon harin ta’addanci a Makarantar Dakarun Soji na Musamman da ke Buni Yadi a Ƙaramar Hukumar Gujba ta Jihar Yobe da sanyin safiyar 8 ga Mayun 2026,” in ji sanarwar.

Ta ƙara da cewa ‘yan sandan, waɗanda suke je makarantar domin samun horo na musamman, sun rasa rayukansu ne lokacin da ‘yan ta’adda suka kai jerin hare-hare a makarantar.

Sanarwar ta ce: “Kazalika jajirtattun dakarun sojin Najeriya da dama sun rasa rayukan a yayin da suke daƙile harin.”

Babban Sufeton ‘yansandan Nijeriya Olatunji Disu ya bayyana ‘yan sandan da aka kashe a matsayin waɗanda suke da “ƙarfin gwiwa da sadaukarwa” da nuna kishin ƙasa a yayin da suka halarci horo kan yaƙi da ta’addanci da wanzar da tsaro.

Ya miƙa saƙon ta’aziyyar ɗaukacin rundunar ‘yansandan Nijeriya ga iyalan jami’an da aka kashe tare da tabbatar musu cewa “ba za a taɓa mantawa da sadaukarwarsu ba.”

A wannan harin ta’addanci, jami’an tsaron Najeriya sun samu nasarar kashe mahara 50.

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, an kashe mayaƙa masu iƙirarin jihadi a lokacin da sojoji suka daƙile wani harin da ƙungiyar ISWAP ta kai a hedikwatar runduna ta 27 a garin Buni Gari da kuma wurin binciken ababen hawa na garin, wanda ke Jihar Yobe.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp