Home Labarai Rundunar ‘Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami’anta 17 a Yobe

Rundunar ‘Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami’anta 17 a Yobe

DCP Anthony Okon Placid

Rundunar ‘Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami’anta 17 a Yobe

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tabbatar da kashe jami’anta 17 a wani harin da ’yan ta’adda suka kai wa wani sansanin horar da dakarun soji na musamman da ke Jihar Yobe.

Wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, DCP Anthony Okon Placid, ya fitar ranar Asabar ta ce an kashe jami’an ne ranar 8 ga watan Mayu.

“Rundunar ‘yan sandan Najeriya tana baƙin cikin sanar da kashe jami’anta 17 yayin da suke aikin bauta wa ƙasa sakamakon harin ta’addanci a Makarantar Dakarun Soji na Musamman da ke Buni Yadi a Ƙaramar Hukumar Gujba ta Jihar Yobe da sanyin safiyar 8 ga Mayun 2026,” in ji sanarwar.

Ta ƙara da cewa ‘yan sandan, waɗanda suke je makarantar domin samun horo na musamman, sun rasa rayukansu ne lokacin da ‘yan ta’adda suka kai jerin hare-hare a makarantar.

Sanarwar ta ce: “Kazalika jajirtattun dakarun sojin Najeriya da dama sun rasa rayukan a yayin da suke daƙile harin.”

Babban Sufeton ‘yansandan Nijeriya Olatunji Disu ya bayyana ‘yan sandan da aka kashe a matsayin waɗanda suke da “ƙarfin gwiwa da sadaukarwa” da nuna kishin ƙasa a yayin da suka halarci horo kan yaƙi da ta’addanci da wanzar da tsaro.

Ya miƙa saƙon ta’aziyyar ɗaukacin rundunar ‘yansandan Nijeriya ga iyalan jami’an da aka kashe tare da tabbatar musu cewa “ba za a taɓa mantawa da sadaukarwarsu ba.”

A wannan harin ta’addanci, jami’an tsaron Najeriya sun samu nasarar kashe mahara 50.

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, an kashe mayaƙa masu iƙirarin jihadi a lokacin da sojoji suka daƙile wani harin da ƙungiyar ISWAP ta kai a hedikwatar runduna ta 27 a garin Buni Gari da kuma wurin binciken ababen hawa na garin, wanda ke Jihar Yobe.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp