Home Labarai Satar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe

Satar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe

Arrest

Satar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe ta kama wasu mutum huɗu da ake zargi da hannu wajen satar kayayyaki a Bankin Bayar da Lamunin Gidaje na Tarayya da ke birnin Gombe.

Wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya raba wa manema labarai a Gombe ta ce ana ci gaba da neman wani daga cikin ababen zargin da ya tsere.

Sanarwar ta bayyana sunayen waɗanda aka kama dukkaninsu matasa da suka fito daga unguwanni daban-daban da ke jihar.

Kakakin ’yan sandan ya ce wani ma’aikacin bankin ne ya shigar da ƙorafi kan lamarin a ranar 15 ga Mayun 2026.

Ma’aikacin bankin ya zargi ɗaya cikin matasan, Umar Sa’idu da haɗa baki da wani mutum mai suna “Rasha”, wanda ya tsere, wajen shiga bankin da ke yankin GRA inda suka yi awon gaba da kayayyakin.

Kayayyakin da aka ce an sace sun haɗa da batir ɗin solar guda huɗu, kwamfutar tafi-da-gidanka nau’in HP, na’urar CCTV decoder da kuma wayar Nokia mai madannai.

Bayan samun rahoton, jami’an ’yan sanda na sashen Pantami suka fara bincike, wanda ya kai ga cafke waɗanda ake zargin tare da kwato wasu daga cikin kayan da aka sace.

A binciken da aka gudanar, an gano batirin solar guda huɗu, kwamfutar HP da kuma na’urar CCTV decoder, yayin da ake ci gaba da neman wanda ya tsere da kuma sauran kayan da aka nema aka rasa.

A wani labarin makamancin wannan, rundunar ta kuma kama wani mutum mai suna Muhammad Bello, mai shekaru 35 daga unguwar Bolari, bisa zargin yunƙurin fashi da makami a yankin Nee GRA da ke kusa da makarantar Pen Resource a Gombe.

’Yan sanda sun ce an kama shi ne bayan samun kiran gaggawa, inda jami’an ofishin Pantami suka kai ɗauki cikin hanzari.

An kuma gano guduma da ake zargin an yi amfani da ita wajen kai harin tare da wani babur nau’in Boxer a hannunsa.

Mutumin da harin ya rutsa da shi ya samu raunuka, inda aka kai shi asibiti domin kula da lafiyarsa kafin daga bisani aka sallame shi.

Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, CP Umar Ahmed Chuso, ya sake jaddada ƙudirin rundunar wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a a faɗin jihar.

Ya kuma buƙaci al’umma da su ci gaba da bai wa jami’an tsaro sahihan bayanai cikin lokaci domin taimaka wa yaƙi da laifuka da inganta tsaro.

Rundunar ta ce yanzu haka bincike na ci gaba da gudana kuma da zarar ta kammala za a gurfanar da waɗanda aka kama a gaban kotu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp