Home Taska An Kashe Matashi Kan Murfin Tayar Adaidaita Sahu a Kano

An Kashe Matashi Kan Murfin Tayar Adaidaita Sahu a Kano

An Kashe Matashi Kan Murfin Tayar Adaidaita Sahu a Kano

 

Wata Kotun Majistare da ke Kano ta bayar da umarnin tsare wani matashi, Auwal Adam, a gidan gyaran hali bisa zargin hannu a kisan wani abokin sana’arsa bayan wata taƙaddama kan murfin tayar babur ɗin Adaidaita Sahu.

Mai Shari’a Sakina Aminu Yusuf ce ta bayar da umarnin tsare matashin bayan ’yan sanda sun gurfanar da shi bisa tuhume-tuhumen haɗa baki da kisan kai.

Sai dai bayan an karanta masa tuhume-tuhumen, matashin da ake zargin ya musanta aikata laifin.

Lauyan masu gabatar da ƙara, A.I. Buhari, ya roƙi kotun da ta ɗage shari’ar domin ba wa masu gabatar da ƙara damar neman shawarar shari’a daga gwamnati.

Alƙaliyar ta amince da buƙatar, inda ta ɗage ci gaba da sauraron shari’ar zuwa ranar 8 ga Satumba, 2026.

’Yan sanda sun yi zargin cewa Auwal Adam da wasu abokansa, waɗanda har yanzu ake nema ruwa a jallo, suna da hannu wajen kisan abokinsu, Aliyu Abubakar Badawa.

A cewar ‘yan sandan, lamarin ya faru ne bayan wata taƙaddama da ta ɓarke tsakanin mutanen kan murfin da ake rufe tayar babur mai ƙafa uku na Adaidaita Sahu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Ƴan Sandan Legas Sun Kama Mutum 4 da Ake Zargi da Fashin Daji, Sun Kwato Wayoyin Hannu 25, Kwamfutoci da Kayan Ado na ZinareRundunar Sojin Ruwa Ta Rusa Wuraren Tace Mai Ba bisa Ka’ida Ba, Ta Kwato Lita 350 na AGO a Rivers2027: Yahaya Bello Ya Tara Masu Daidaita Ayyuka na A4A a Arewa ta Tsakiya Domin sake Zaban TinubuSojoji Sun Kama Mutum 2 da ake Zargi da Taimakawa Ƴan Ta’adda, Sun Kwace Kayayyakin Babur a YobePDP Ta Yi Gargadi Kan Zargin Tattara Katunan Zabe PVC da Bayanan Asusun Banki a GombeRundunar Sojojin Najeriya ta Sauya Manyan Janarori Zuwa Muhimman Mukamai na Aiki da DabaruHukumar INEC za ta ƙaddamar da Na’urar Bibiyar shirye-shiryen Zaɓen 2027 kai TsayeDaliban Tallafin Horarwa na Prnigeria Sun Ziyarci Emirate FM, Sun Samu Kyawawan Bayani Kan Watsa Labarai na DijitalNSCIA ta yi Allah Wadai da Nuna Bambancin Addini a Ci gaba da Tsare El-RufaiSarkin Ilorin Ya Yaba da Tallafin Horarwa na PRNigeria Wajen Shirya Masu Watsa Labarai na Nan GabaNDLEA Ta Kama Mai Safarar Hodar Iblis da ake Zargi da Laifi Akan Jigilar Kaya a Saudiyya, ta Kuma Kama Kwayoyi Masu Yaduwa Sama Da Miliyan 2Gwamnatin Tarayya ta Yaba da N5.41 Trillion da Kwastam ta Tara, Ta Nemi a bi Ka'idojin Duniya Hukumar Kwastam Ta Naɗa DCG, ACG 5, ta yi Nazarin Yadda aka Samu Kuɗin Shiga2027: HURIWA Ta Bukaci Ƴan Sanda da su Gurfanar da Ƴan Siyasa Kan Zargin Kalamai Masu Tada HankaliSojoji Sun Tarwatsa Maboyar Ƴan Ta'adda, Sun Kwace Bindigogin AK-47 a Sokoto 
X whatsapp