Home Taska An Kashe Matashi Kan Murfin Tayar Adaidaita Sahu a Kano

An Kashe Matashi Kan Murfin Tayar Adaidaita Sahu a Kano

An Kashe Matashi Kan Murfin Tayar Adaidaita Sahu a Kano

 

Wata Kotun Majistare da ke Kano ta bayar da umarnin tsare wani matashi, Auwal Adam, a gidan gyaran hali bisa zargin hannu a kisan wani abokin sana’arsa bayan wata taƙaddama kan murfin tayar babur ɗin Adaidaita Sahu.

Mai Shari’a Sakina Aminu Yusuf ce ta bayar da umarnin tsare matashin bayan ’yan sanda sun gurfanar da shi bisa tuhume-tuhumen haɗa baki da kisan kai.

Sai dai bayan an karanta masa tuhume-tuhumen, matashin da ake zargin ya musanta aikata laifin.

Lauyan masu gabatar da ƙara, A.I. Buhari, ya roƙi kotun da ta ɗage shari’ar domin ba wa masu gabatar da ƙara damar neman shawarar shari’a daga gwamnati.

Alƙaliyar ta amince da buƙatar, inda ta ɗage ci gaba da sauraron shari’ar zuwa ranar 8 ga Satumba, 2026.

’Yan sanda sun yi zargin cewa Auwal Adam da wasu abokansa, waɗanda har yanzu ake nema ruwa a jallo, suna da hannu wajen kisan abokinsu, Aliyu Abubakar Badawa.

A cewar ‘yan sandan, lamarin ya faru ne bayan wata taƙaddama da ta ɓarke tsakanin mutanen kan murfin da ake rufe tayar babur mai ƙafa uku na Adaidaita Sahu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
An Kashe Matashi Kan Murfin Tayar Adaidaita Sahu a KanoMutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14
X whatsapp