Home Taska Mabiya Addinai Biyu a Najeriya Sun Sanya Hannu Kan Sabuwar Yarjejeniya

Mabiya Addinai Biyu a Najeriya Sun Sanya Hannu Kan Sabuwar Yarjejeniya

Mabiya Addinai Biyu a Najeriya Sun Sanya
Hannu Kan Sabuwar Yarjejeniya

 

Shugabannin addinin Musulunci da Kiristoci fiye da 50 ne suka rattaba hannu kan wata yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin mabiya addinan biyu a Najeriya,

An ƙaddamar da wata sabuwar ƙungiya da za ta mayar da hankali wajen inganta fahimtar juna da zaman lafiya tsakanin addinai, a taron da ƙungiyar Musulmi ta Duniya da ke da hedikwata a Saudiyya ta shirya a Abuja.

Yarjejeniyar ta zo ne watanni bayan da Shugaban Amurka Donald Trump ya zargi Najeriya da gaza kare Kiristoci daga hare-haren ƙungiyoyin masu ikirarin jihadi, tare da yin barazanar daukar matakin soji kan ƙasar.

Sai dai ba a yi magana kan kalaman Trump ba a taron da aka sanya hannu kan yarjejeniyar.

Sakatare Janar na ƙungiyar Musulmi ta Duniya, Mohammad Al-Issa, yana cewa dukkanin mabiya addinan biyu na maraba da wannan tsari da ya ce ya “buɗe sabon shafi”.

Shugabannin Musulmi da Kiristocin da suka halarci taron sun ce yarjejeniyar za ta iya taimakawa wajen rage kalaman ƙiyayya da rarrabuwar kawuna.

Mataimakin shugaban Majalisar Dattawa, Barau Jibrin, wanda ya wakilci Shugaba Bola Tinubu wajen bikin, ya ce gwamnati ta kuduri aniyar ganin Najeriya ta ci gaba da kasancewa dunƙulalliyar ƙasa duk da bambance-bambancen da ke tsakaninta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Ƴan Sandan Legas Sun Kama Mutum 4 da Ake Zargi da Fashin Daji, Sun Kwato Wayoyin Hannu 25, Kwamfutoci da Kayan Ado na ZinareRundunar Sojin Ruwa Ta Rusa Wuraren Tace Mai Ba bisa Ka’ida Ba, Ta Kwato Lita 350 na AGO a Rivers2027: Yahaya Bello Ya Tara Masu Daidaita Ayyuka na A4A a Arewa ta Tsakiya Domin sake Zaban TinubuSojoji Sun Kama Mutum 2 da ake Zargi da Taimakawa Ƴan Ta’adda, Sun Kwace Kayayyakin Babur a YobePDP Ta Yi Gargadi Kan Zargin Tattara Katunan Zabe PVC da Bayanan Asusun Banki a GombeRundunar Sojojin Najeriya ta Sauya Manyan Janarori Zuwa Muhimman Mukamai na Aiki da DabaruHukumar INEC za ta ƙaddamar da Na’urar Bibiyar shirye-shiryen Zaɓen 2027 kai TsayeDaliban Tallafin Horarwa na Prnigeria Sun Ziyarci Emirate FM, Sun Samu Kyawawan Bayani Kan Watsa Labarai na DijitalNSCIA ta yi Allah Wadai da Nuna Bambancin Addini a Ci gaba da Tsare El-RufaiSarkin Ilorin Ya Yaba da Tallafin Horarwa na PRNigeria Wajen Shirya Masu Watsa Labarai na Nan GabaNDLEA Ta Kama Mai Safarar Hodar Iblis da ake Zargi da Laifi Akan Jigilar Kaya a Saudiyya, ta Kuma Kama Kwayoyi Masu Yaduwa Sama Da Miliyan 2Gwamnatin Tarayya ta Yaba da N5.41 Trillion da Kwastam ta Tara, Ta Nemi a bi Ka'idojin Duniya Hukumar Kwastam Ta Naɗa DCG, ACG 5, ta yi Nazarin Yadda aka Samu Kuɗin Shiga2027: HURIWA Ta Bukaci Ƴan Sanda da su Gurfanar da Ƴan Siyasa Kan Zargin Kalamai Masu Tada HankaliSojoji Sun Tarwatsa Maboyar Ƴan Ta'adda, Sun Kwace Bindigogin AK-47 a Sokoto 
X whatsapp