Home Taska Safarar Miyagun Kwayoyi: NDLEA ta yi Martani ga Jawabin Sifeto Janar na...

Safarar Miyagun Kwayoyi: NDLEA ta yi Martani ga Jawabin Sifeto Janar na ‘Yan Sanda Kan Abba Kyari

Safarar Miyagun Kwayoyi: NDLEA ta yi Martani ga Jawabin Sifeto Janar na ‘Yan Sanda Kan Abba Kyari

 

Kakakin hukumar NDLEA ya yi martani bisa kalaman hukumar yan sanda na zargin boye jami’ansu da sukay aiki tare da Abba Kyari.

Jami’n hukumar ya yi alkawarin cewa ana kammala bincike kan lamarin za’a bayyanawa yan Najeriya.

Hukumar hana amfani da miyagun kwayoyi a Najeriya NDLEA ta yi martani da jawabin Sifeto Janar na yan sanda inda yayi kira ga a hukunta jami’an hukumar da suke taimakawa wajen shigo da hodar Iblis Najeriya.

Zaku tuna cewa a ranar Litinin hukumar NDLEA ta garkame dakataccen DCP na yan sanda, Abba Kyari, kan laifin safarar hodar Iblis mai nauyin kilo 25.

Wannan ya biyo bayan damkeshi da hukumar yan sanda tayi kuma ta mikasa tare da sauran yan sandan dake harkallar tare ga hukumar NDLEA.

Sifeto Janar na yan sanda, IGP Usman Baba Alkali, ya yi kira ga Shugaban hukumar hana fasa kwabrin muggan kwayoyi, Janar Buba Marwa (mrty) ya damke jami’ansa dake taimakawa masu safarar kwaya tare da Abba Kyari.

Daily Trust ta ruwaito kakakin hukumar, Femi Babafemi, da cewa hukumar ba zata yi wani rufa-rufa ba, ko wanene sai an tona masa asiri.

Yayinda aka tambayesa shin me yasa ba’a ambaci sunayen jami’an NDLEA da sukayi safarar tare da Abba Kyari ba, Babafemi yace hukumar ba zata boye kowa ba.

Yace:

“Bayan yin abinda ya dace, wani irin rufa-rufa zamu yi? Duk wanda aka kama da laifi zai fuskanci fushin hukuma.Kuma wannan ne ra’ayin Shugaban NDLEA, Birgediya Janar Buba Marwa.”

“Muna fatan yan Najeriya su bar hukumar ta kammala aikinta kuma muna tabbatarwa yan Najeriya cewa zamu bayyana musu sakamakon binciken.”

Mu muka kama yan kwaya ba NDLEA ba

Dazu mun kawo muku rahoto IGP inda yace jami’an yan sanda ne suka kamasu ba jami’an NDLEA ba, jami’an NDLEA sun barsu sun wuce saboda an basu cin hanci.

A cewarsa, masu safarar kwayar na turawa jami’an NDLEA hotunansu kafin su isa tashar jirgin sama, saboda haka suna ganinsu suke barinsu su wuce.

Yace:

“Jami’an NDLEA sun barsu sun wuce saboda tun kafin su isa Akwa Ibom an turo musu hotunansu, yayinda suke kokarin fita daga tashar jirgin da kwayoyi ne yan sanda suka kamasu.”

“Saboda haka, Sifeto Janar na yan sanda ya bukaci Shugaban hukumar hana fasa kwabrin kwayoyi ya tabbatar ya damke jami’an hukumarsa dake hada baki da yan kwayan kuma ya gudanar da bincike.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp