Home Taska Safarar Miyagun Kwayoyi: NDLEA ta yi Martani ga Jawabin Sifeto Janar na...

Safarar Miyagun Kwayoyi: NDLEA ta yi Martani ga Jawabin Sifeto Janar na ‘Yan Sanda Kan Abba Kyari

Safarar Miyagun Kwayoyi: NDLEA ta yi Martani ga Jawabin Sifeto Janar na ‘Yan Sanda Kan Abba Kyari

 

Kakakin hukumar NDLEA ya yi martani bisa kalaman hukumar yan sanda na zargin boye jami’ansu da sukay aiki tare da Abba Kyari.

Jami’n hukumar ya yi alkawarin cewa ana kammala bincike kan lamarin za’a bayyanawa yan Najeriya.

Hukumar hana amfani da miyagun kwayoyi a Najeriya NDLEA ta yi martani da jawabin Sifeto Janar na yan sanda inda yayi kira ga a hukunta jami’an hukumar da suke taimakawa wajen shigo da hodar Iblis Najeriya.

Zaku tuna cewa a ranar Litinin hukumar NDLEA ta garkame dakataccen DCP na yan sanda, Abba Kyari, kan laifin safarar hodar Iblis mai nauyin kilo 25.

Wannan ya biyo bayan damkeshi da hukumar yan sanda tayi kuma ta mikasa tare da sauran yan sandan dake harkallar tare ga hukumar NDLEA.

Sifeto Janar na yan sanda, IGP Usman Baba Alkali, ya yi kira ga Shugaban hukumar hana fasa kwabrin muggan kwayoyi, Janar Buba Marwa (mrty) ya damke jami’ansa dake taimakawa masu safarar kwaya tare da Abba Kyari.

Daily Trust ta ruwaito kakakin hukumar, Femi Babafemi, da cewa hukumar ba zata yi wani rufa-rufa ba, ko wanene sai an tona masa asiri.

Yayinda aka tambayesa shin me yasa ba’a ambaci sunayen jami’an NDLEA da sukayi safarar tare da Abba Kyari ba, Babafemi yace hukumar ba zata boye kowa ba.

Yace:

“Bayan yin abinda ya dace, wani irin rufa-rufa zamu yi? Duk wanda aka kama da laifi zai fuskanci fushin hukuma.Kuma wannan ne ra’ayin Shugaban NDLEA, Birgediya Janar Buba Marwa.”

“Muna fatan yan Najeriya su bar hukumar ta kammala aikinta kuma muna tabbatarwa yan Najeriya cewa zamu bayyana musu sakamakon binciken.”

Mu muka kama yan kwaya ba NDLEA ba

Dazu mun kawo muku rahoto IGP inda yace jami’an yan sanda ne suka kamasu ba jami’an NDLEA ba, jami’an NDLEA sun barsu sun wuce saboda an basu cin hanci.

A cewarsa, masu safarar kwayar na turawa jami’an NDLEA hotunansu kafin su isa tashar jirgin sama, saboda haka suna ganinsu suke barinsu su wuce.

Yace:

“Jami’an NDLEA sun barsu sun wuce saboda tun kafin su isa Akwa Ibom an turo musu hotunansu, yayinda suke kokarin fita daga tashar jirgin da kwayoyi ne yan sanda suka kamasu.”

“Saboda haka, Sifeto Janar na yan sanda ya bukaci Shugaban hukumar hana fasa kwabrin kwayoyi ya tabbatar ya damke jami’an hukumarsa dake hada baki da yan kwayan kuma ya gudanar da bincike.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp