Home SIYASA Kotu ta Bawa Jam’iyyar APC Ranar da Zata Gudanar da Babban Taronta...

Kotu ta Bawa Jam’iyyar APC Ranar da Zata Gudanar da Babban Taronta na Kasa

Kotu ta Bawa Jam’iyyar APC Ranar da Zata Gudanar da Babban Taronta na Kasa

Wata babbar kotu a Abuja babban birnin tarayyar Najeriya ta yanke hukuncin kyale jam’iyyar APC mai mulkin Najeriya ta gudanar da babban taronta na kasa a ranar 26 ga watan Maris na wannan shekarar.

A ranar Juma’a alkalin kotun, Mai shari’a Bello kawu ya yanke hukunci cewa ‘ya’yan jam’iyyar ba su da hurumin kai kararta.

Ya ce wani umarnin Kotun Kolin Najeriya kan wani batu irin wannan ya sha gaban wanda babbar kotun ta fitar na 18 ga watan Nuwambar bara.

Kotun ta daga zamanta zuwa ranar 30 ga wannan watan na Maris domin ci gaba da sauraren karar.

Wani mamba a jam’iyyar mai suna Salisu Umoru ne ya shigar da kara inda yake so kotun ta hana jam’iyyar ta APC da gwamna Mai Mala Buni da kuma hukumar zabe mai zaman kanta ta Najeriya, INEC su shirya babban taro na kasa na jam’iyyar har sai bayan an kammala sauraren karar da ya shigar.

Yadda matsalar ta samo asali
Yayin da damuwa ke karuwa tsakanin manyan jami’an jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya, wata kotu za ta yanke hukunci kan karar da aka shigar a gabanta wadda ake neman a soke wani umarni da ya hana jam’iyyar gudanar da babban taronta na kasa ranar 26 ga watan Maris.

Cikin mako biyun da suka gabata wasu gwamnonin jihohin kasar sun yi kokarin sauya shugabannin jam’iyyar, matakin da ya janyo karuwar fargaba da matsaloli ga ‘ya’yan jam’iyyar.

Sau uku ana cin karo da matsaloli yayin da ‘ya’yan jam’iyyar ke kokarin samar da shugabanin da za su karbi ragamar jam’iyyar daga hannun kwamitin riko karkashin gwamnan jihar Yobe Mai Mala Buni.

Karar da aka shigar a gaban kotun wanda ke son a kawar da umarnin kotun na ranar 18 ga watan Nuwamba 2021 ya gamu da cikas bayan da wasu lauyoyi biyu, Shuaibu Aruwan (SAN) da Michael Adoyi suka sanar da kotun cewa sune ke wakiltar jam’iyyar.

Bayan da kotun ta zauna ranar Talatar da ta gabata, Mista Aruwan ya sanar da kotun cewa ya sami wata wasika daga jam’iyyar APC da ta tabbatar da nadinsa a matsayin lauyan jam’iyyar a wannan shari’ar kamar yadda kotun ta umarci a yi.

Daga nan sai ya nemi kotun ta kawar da umarnin kotun na farko saboda rashin hurumi.

Amma lauya Mike Enahoro-Eba, wanda shi ke wakiltar wadanda suka shigar da karar ya ki amincewa da wannan bukatar, yana cewa dokokin kotun sun bukaci a bayar da kwanaki bakwai domin wadanda ake kalubalanta su sami damar mayar da martani.

Daga nan ne alkalin da ke sauraron karar, Mai shari’a Bello Kawu ya ajiye ranar Juma’a 18 ga watan Maris domin yanke hukunci.

Ganin muhimmancin wannan ranar ga jam’iyyar ta APC, masana siyasar Najeriya na cewa rashin warware wannan matsalar na iya haifar da babban kalubale ga jam’iyyar ta APC mai mulkin Najeriya ganin cewa kasa da shekara guda ya rage a gudanar da babban zabe a kasar, wanda ‘yan kasar za su zabi sabon shugaban kasa da gwamnonin yawancin jihohi da kuma ‘yan majalisun tarayya da jihohin kasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp