Home SIYASA Bola Tinubu ya Bawa LASU Gudumawar Naira 1bn

Bola Tinubu ya Bawa LASU Gudumawar Naira 1bn

Bola Tinubu ya Bawa LASU Gudumawar Naira 1bn

Tsohon gwamnan jihar Legas, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya ba da gudummawar Naira biliyan 1 don gina cibiyar jagoranci a jami’ar jihar ta Legas.

Mataimakin shugaban jami’ar ta jihar Legas ne ya sanar da bayar da gudummawar a lokacin taron yaye dalibai na jami’ar karo na 25.

Tinubu ya jagoranci al’amuran jihar Legas daga 1999 zuwa 2007 kuma tun daga nan ya zama shugaban jam’iyyar APC na kasa.

Dan takarar shugaban kasa kuma jigo a jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Tinubu, ya baiwa jami’ar jihar Legas (LASU), gudunmawar kudi don gina wata cibiyar bunkasa ilimin jagoranci da ya kai Naira biliyan 1.

Mataimakin shugaban jami’ar LASU, Farfesa Ibiyemi Olatunji-Bello ne ya sanar da bayar da gudummawar a taron lacca yaye dalibai karo na 25 a ranar Alhamis, 24 ga watan Maris.

Jaridar Leadership ta ruwaito cewa, mataimakin gwamnan jihar Legas Dr. Obafemi Hamzat ne ya wakilci Tinubu a wajen taron.

Da yake magana ta bakin Hamzat, Tinubu ya bukaci gwamnati ta tallafa wa masana’antun dabaru da za su dauki matasa aiki tare da samar da ayyukan yi.

Ya ce tallafin da gwamnati ke bayarwa na kere-kere da masana’antu zai kara bude kofa ga fara sana’o’in da kasuwanci tsakanin matasa.

A fadinsa:

“Manufofin masana’antu da ayyukan yi na kasa dole ne su yi tashi daga shafukan takardu su zo cikin rayuwa ta zahiri.

“Wannan zai taimaka wajen gyara al’umma don inganta tattalin arzikin matasa a cikinta.

“Muna bukatar sabuwar hanya mai gamsarwa, hanyar da za ta ba ku dama mai kyau a kyakkyawar damar samun wadata mai dorewa.”

Wadanda suka halarci taron a jihar Legas

Wadanda suka halarci bikin sun hada da Gwamna Abdullahi Ganduje na jihar Kano, da wakilan gwamna Aminu Masari na jihar Katsina, da mataimakin gwamnan jihar Borno, da mataimakan shugabannin jami’o’i daban-daban na kasar nan.

Haka kuma, akwai tsoffin gwamnonin jihar Legas biyu, Gimbiya Adejoke Adefulire da Dr Idiat Adegbule, kamar yadda Independent ta ruwaito.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp