Home Taska kudaden Paris Club: Kotu ta yi Watsi da Karar da Manyan Lauyoyin...

kudaden Paris Club: Kotu ta yi Watsi da Karar da Manyan Lauyoyin Gwamnatin Jahohi 36 Suka Shigar Kan Gwamnatin Tarayya

kudaden Paris Club: Kotu ta yi Watsi da Karar da Manyan Lauyoyin Gwamnatin Jahohi 36 Suka Shigar Kan Gwamnatin Tarayya

 

Abuja- Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta yi watsi da karar da manyan lauyoyin gwamnatin jihohi 36 suka shigar kan gwamnatin tarayya.

A cikin karar, jihohin na kalubalantar shirin cire dala miliyan 418 daga asusun tarayya don biyan basussukan da wasu masu ba da shawara na jihohi da kananan hukumomi ke bin su dangane da kudaden Paris Club.

Mai shari’a Inyang Ekwo ya yi watsi da karar ne a wani hukuncin da ya yanke a ranar Juma’a, yana mai cewa manyan lauyoyin ba su kawo isassun shaidun da za su ba su zamsar da kotu ba.

Kafar yada labarai ta Channels Tv ta ruwaito cewa, alkalin ya ce babu wata kwakkwarar hujja da ta nuna cewa gwamnonin jihohin 36 sun amince da shigar da karar.

A cewar alkalin, an samar da ofishin babban Lauyan Jiha ne a karkashin sashe na 195 na kundin tsarin mulkin kasar na 1999, sannan kuma AG na jiha gwamna ne ke nada shi, wanda hakan ya sa AG ya zama wanda ke aiki a karkashin ikon wani gwamna.

Ya ci gaba da cewa jayayyar da masu shigar da kara suka yi na cewa ba bangaren shari’a ba ne, bai kai ga ci ba, domin kungiyar gwamnonin Najeriya da kungiyar kananan hukumomi sun shiga cikin karar.

Kotun ta ci gaba da cewa wadanda suka shigar da karar sun amince da akwai bashin da ake bi, inda suka dage cewa shigar da karar wata dabara ce ta kalubalantar bashin da ake bi.

Mai shari’a Ekwo ya bayyana cewa matakin da masu shigar da karar suka dauka na nuna cin zarafin tsarin shari’a ne, inda daga bisani ya yi watsi da karar saboda rashin cancantarta.

Karin bayani na nan tafe…

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp