Home Taska kudaden Paris Club: Kotu ta yi Watsi da Karar da Manyan Lauyoyin...

kudaden Paris Club: Kotu ta yi Watsi da Karar da Manyan Lauyoyin Gwamnatin Jahohi 36 Suka Shigar Kan Gwamnatin Tarayya

kudaden Paris Club: Kotu ta yi Watsi da Karar da Manyan Lauyoyin Gwamnatin Jahohi 36 Suka Shigar Kan Gwamnatin Tarayya

 

Abuja- Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta yi watsi da karar da manyan lauyoyin gwamnatin jihohi 36 suka shigar kan gwamnatin tarayya.

A cikin karar, jihohin na kalubalantar shirin cire dala miliyan 418 daga asusun tarayya don biyan basussukan da wasu masu ba da shawara na jihohi da kananan hukumomi ke bin su dangane da kudaden Paris Club.

Mai shari’a Inyang Ekwo ya yi watsi da karar ne a wani hukuncin da ya yanke a ranar Juma’a, yana mai cewa manyan lauyoyin ba su kawo isassun shaidun da za su ba su zamsar da kotu ba.

Kafar yada labarai ta Channels Tv ta ruwaito cewa, alkalin ya ce babu wata kwakkwarar hujja da ta nuna cewa gwamnonin jihohin 36 sun amince da shigar da karar.

A cewar alkalin, an samar da ofishin babban Lauyan Jiha ne a karkashin sashe na 195 na kundin tsarin mulkin kasar na 1999, sannan kuma AG na jiha gwamna ne ke nada shi, wanda hakan ya sa AG ya zama wanda ke aiki a karkashin ikon wani gwamna.

Ya ci gaba da cewa jayayyar da masu shigar da kara suka yi na cewa ba bangaren shari’a ba ne, bai kai ga ci ba, domin kungiyar gwamnonin Najeriya da kungiyar kananan hukumomi sun shiga cikin karar.

Kotun ta ci gaba da cewa wadanda suka shigar da karar sun amince da akwai bashin da ake bi, inda suka dage cewa shigar da karar wata dabara ce ta kalubalantar bashin da ake bi.

Mai shari’a Ekwo ya bayyana cewa matakin da masu shigar da karar suka dauka na nuna cin zarafin tsarin shari’a ne, inda daga bisani ya yi watsi da karar saboda rashin cancantarta.

Karin bayani na nan tafe…

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp