Home Taska kudaden Paris Club: Kotu ta yi Watsi da Karar da Manyan Lauyoyin...

kudaden Paris Club: Kotu ta yi Watsi da Karar da Manyan Lauyoyin Gwamnatin Jahohi 36 Suka Shigar Kan Gwamnatin Tarayya

kudaden Paris Club: Kotu ta yi Watsi da Karar da Manyan Lauyoyin Gwamnatin Jahohi 36 Suka Shigar Kan Gwamnatin Tarayya

 

Abuja- Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta yi watsi da karar da manyan lauyoyin gwamnatin jihohi 36 suka shigar kan gwamnatin tarayya.

A cikin karar, jihohin na kalubalantar shirin cire dala miliyan 418 daga asusun tarayya don biyan basussukan da wasu masu ba da shawara na jihohi da kananan hukumomi ke bin su dangane da kudaden Paris Club.

Mai shari’a Inyang Ekwo ya yi watsi da karar ne a wani hukuncin da ya yanke a ranar Juma’a, yana mai cewa manyan lauyoyin ba su kawo isassun shaidun da za su ba su zamsar da kotu ba.

Kafar yada labarai ta Channels Tv ta ruwaito cewa, alkalin ya ce babu wata kwakkwarar hujja da ta nuna cewa gwamnonin jihohin 36 sun amince da shigar da karar.

A cewar alkalin, an samar da ofishin babban Lauyan Jiha ne a karkashin sashe na 195 na kundin tsarin mulkin kasar na 1999, sannan kuma AG na jiha gwamna ne ke nada shi, wanda hakan ya sa AG ya zama wanda ke aiki a karkashin ikon wani gwamna.

Ya ci gaba da cewa jayayyar da masu shigar da kara suka yi na cewa ba bangaren shari’a ba ne, bai kai ga ci ba, domin kungiyar gwamnonin Najeriya da kungiyar kananan hukumomi sun shiga cikin karar.

Kotun ta ci gaba da cewa wadanda suka shigar da karar sun amince da akwai bashin da ake bi, inda suka dage cewa shigar da karar wata dabara ce ta kalubalantar bashin da ake bi.

Mai shari’a Ekwo ya bayyana cewa matakin da masu shigar da karar suka dauka na nuna cin zarafin tsarin shari’a ne, inda daga bisani ya yi watsi da karar saboda rashin cancantarta.

Karin bayani na nan tafe…

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp