Home SIYASA Kotun Koli a Najeriya ta Tabbatar da Soke Rajistar Jam’iyyun Siyasa 22

Kotun Koli a Najeriya ta Tabbatar da Soke Rajistar Jam’iyyun Siyasa 22

Kotun Koli a Najeriya ta Tabbatar da Soke Rajistar Jam’iyyun Siyasa 22

Abuja Kotun koli a Najeriya ta tabbatar da hukuncin soke rajistar wasu jam’iyyun siyasa 22 da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta yi a shekarun baya.

Jam’iyyu 22 na daga cikin 74 da INEC ta soke rajistarsu a 2020 sakamakon rashin tabuka abin a zo a gani a zaben 2019, inji rahoton Leadership.

Mai shari’a Ejembi Eko na kotun koli ya yi watsi da hukuncin da kotun daukaka kara da ke Abuja ta yanke, wanda ya kalubalanci matsayar INEC na soke rajistar jam’iyyun.

Mai shari’a Eko ya bayyana cewa, Kotun daukaka kara a karan kanta ta tabo batun rashin sauraron shari’ar adalci ga bangaren jam’iyyun 22 da aka soke, inda ta cimma matsaya ba tare da jin ta bakin wasu bangarori a kan lamarin ba.

A cewar mai shari’a:

“Wannan bukata da INEC ta nema ya dace kuma an amince da hakan. Hukuncin kotun da ke kasa an yi watsi da shi.”

Kotun kolin ta bayyana cewa kotun daukaka kara ya fitar da batun sauraron karar ne daga duban bukatar daukaka kara da jam’iyyun siyasa suka shigar amma ta ki yin abin da ya dace domin yin adalci ga wasu da lamarin ya shafa.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp