Home Taska Jami’an Ukraine 300 ne Suka Rasa Rayukansu a Harin da Rasha ta...

Jami’an Ukraine 300 ne Suka Rasa Rayukansu a Harin da Rasha ta Kai Birnin Mariupol

Jami’an Ukraine 300 ne Suka Rasa Rayukansu a Harin da Rasha ta Kai Birnin Mariupol

Mun sami karin bayanai kan harin sama da dakarun Rasha suka kai a birnin Mariupol na kudancin Ukraine.

Kawo yanzu, ba a san yawan wadanda suka mutu daga harin ba saboda ci gaba da kai hare-hare babu kakkautawa da sojojin Rasha ke yi kan birnin.

Amma jami’an Ukraine a yanzu sun ce kimanin mutum 300 ne suka rasa rayukansu yayin wancan harin, wanda ya fada kan wani ginin gidan wasannin kwaikwayo, inda daruruwan ‘yan Ukraine ke neman mafaka.

Jami’an Ukraine na cewa Rasha ce ta kai harin, sai dai Rashar ta musanta ikirarin nasu.

Ofishin Magajin Garin Mariupol ya ce “Daga bayanan da shaidu suka sanar da mu, kimanin mutum 300 ne suka halaka a ginin Drama Theatre na Mariupol wanda ya biyo bayan hare-hare da jiragen yakin Rasha suka kai.”

Sai dai kafofin sadarwa da birnin na Mariupol sun kasance ‘yan kalilan, saboda haka ne babu yadda za a iya tantance sahihancin rahotannin da ke fitowa daga can.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp