Home Taska Jami’an Ukraine 300 ne Suka Rasa Rayukansu a Harin da Rasha ta...

Jami’an Ukraine 300 ne Suka Rasa Rayukansu a Harin da Rasha ta Kai Birnin Mariupol

Jami’an Ukraine 300 ne Suka Rasa Rayukansu a Harin da Rasha ta Kai Birnin Mariupol

Mun sami karin bayanai kan harin sama da dakarun Rasha suka kai a birnin Mariupol na kudancin Ukraine.

Kawo yanzu, ba a san yawan wadanda suka mutu daga harin ba saboda ci gaba da kai hare-hare babu kakkautawa da sojojin Rasha ke yi kan birnin.

Amma jami’an Ukraine a yanzu sun ce kimanin mutum 300 ne suka rasa rayukansu yayin wancan harin, wanda ya fada kan wani ginin gidan wasannin kwaikwayo, inda daruruwan ‘yan Ukraine ke neman mafaka.

Jami’an Ukraine na cewa Rasha ce ta kai harin, sai dai Rashar ta musanta ikirarin nasu.

Ofishin Magajin Garin Mariupol ya ce “Daga bayanan da shaidu suka sanar da mu, kimanin mutum 300 ne suka halaka a ginin Drama Theatre na Mariupol wanda ya biyo bayan hare-hare da jiragen yakin Rasha suka kai.”

Sai dai kafofin sadarwa da birnin na Mariupol sun kasance ‘yan kalilan, saboda haka ne babu yadda za a iya tantance sahihancin rahotannin da ke fitowa daga can.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp