Home SIYASA Maslaha za a Bai wa Fifiko Wajen Zaɓan Shugaban APC – Garba...

Maslaha za a Bai wa Fifiko Wajen Zaɓan Shugaban APC – Garba Shehu

Maslaha za a Bai wa Fifiko Wajen Zaɓan Shugaban APC – Garba Shehu

 

Ga alama batun zaɓen shugaban APC ta hanyar maslaha zai yi wuya, inda wasu ƴan takara har zuwa ranar babban taron jam’iyyar ba su janye ba.

Jam’iyyar APC dai ta nuna cewa tsarin daidaitawa ko maslaha ne tsarin da ta fi so wajen zaɓar shugabanninta.

Shugaba Buhari ma ya nuna tsarin maslaha ko daidaitawa tsakanin ƴan takara ne yake goyon baya.

Mai magana da yawun shugaban kasa, Malam Garba Shehu, kuma jami`i a kwamitin yada labarai na babban taron APC ya ce maslaha za a bai wa fifiko, kuma abin da jiga-jigan APC suka kashe dare suna yi ke nan, suna lallashin sauran `yan takara domin su mara wa mutum guda. Har ma an ba da umurnin jam`iyya ta mayar musu da kudin da suka kashe wajen sayen fam.

Mutum tara ne suka nuna sha`awar takarar shugabancin jam`iyyar, kuma har zuwa safiyar Asabar ranar babban taron APC babu labarin janyewar wasu ƴan takarar da ke neman shugabancin jam’iyyar.

Tun tuni rahotanni ke cewa tsohon gwamnan jihar Nasarawa, Senata Abdullahi Adamu ne shugban kasa da jiga-jigan APC ke goyon baya don zama shugaban jam`iyya, kuma har yanzu fadar shugaban kasa ba ta musanta ba.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp