Home SIYASA Maslaha za a Bai wa Fifiko Wajen Zaɓan Shugaban APC – Garba...

Maslaha za a Bai wa Fifiko Wajen Zaɓan Shugaban APC – Garba Shehu

Maslaha za a Bai wa Fifiko Wajen Zaɓan Shugaban APC – Garba Shehu

 

Ga alama batun zaɓen shugaban APC ta hanyar maslaha zai yi wuya, inda wasu ƴan takara har zuwa ranar babban taron jam’iyyar ba su janye ba.

Jam’iyyar APC dai ta nuna cewa tsarin daidaitawa ko maslaha ne tsarin da ta fi so wajen zaɓar shugabanninta.

Shugaba Buhari ma ya nuna tsarin maslaha ko daidaitawa tsakanin ƴan takara ne yake goyon baya.

Mai magana da yawun shugaban kasa, Malam Garba Shehu, kuma jami`i a kwamitin yada labarai na babban taron APC ya ce maslaha za a bai wa fifiko, kuma abin da jiga-jigan APC suka kashe dare suna yi ke nan, suna lallashin sauran `yan takara domin su mara wa mutum guda. Har ma an ba da umurnin jam`iyya ta mayar musu da kudin da suka kashe wajen sayen fam.

Mutum tara ne suka nuna sha`awar takarar shugabancin jam`iyyar, kuma har zuwa safiyar Asabar ranar babban taron APC babu labarin janyewar wasu ƴan takarar da ke neman shugabancin jam’iyyar.

Tun tuni rahotanni ke cewa tsohon gwamnan jihar Nasarawa, Senata Abdullahi Adamu ne shugban kasa da jiga-jigan APC ke goyon baya don zama shugaban jam`iyya, kuma har yanzu fadar shugaban kasa ba ta musanta ba.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp