Home Taska Abu Mai Fashewa ya Fashe a Yakin Rigasa da ke Jahar Kaduna

Abu Mai Fashewa ya Fashe a Yakin Rigasa da ke Jahar Kaduna

Abu Mai Fashewa ya Fashe a Yakin Rigasa da ke Jahar Kaduna

 

Mazauna yankin rigasa sun shiga ruɗani, yayin da wani abu mai fashewa ya fashe a daren Juma’a kusa da mai P.O.S, wajen wani masallaci.

Lamarin ya ritsa da mutane uku, wanda daga cikinsu mai P.O.S din ne yafi samun matsanancin rauni, daga bisani aka garzaya dashi asibiti.

Hakan ya faru ne, bayan wasu makonni da kwamishinan kula da lamurran cikin gida ya bukaci jama’a da su sa ido, duba da rahoton yadda ƴan ta’adda ke shirin dasa abubuwa masu fashewa a wurare.

Mazauna yankin Danmani na Rigasa, cikin ƙaramar hukumar Igabi dake jihar Kaduna sun shiga tashin hankali bayan fashewar wani abu a daren juma’a.

Lamarin ya auku ne, kusa da shagon P.O.S, wajen masallacin Abubakar Sadiq, kamar yadda mazauna yankin suka bayyana.

Daily Trust ta tattaro yadda aka ga wani abu mai fashewa kusa da wani babur, wanda ake tunanin mallakin mai shagon P.O.S din ne a yankin.

Wani ɗan sa kan yankin, wanda ya bukaci a sakaya sunansa, ya labarta yadda fashewar abun ya raunata mai P.O.S din, wanda daga bisani aka garzaya dashi asibiti.

“An garzaya da mutumin asibiti don nema masa lafiya, saboda kafafunsa da ƙunbunan kafafun sun samu rauni matuka. Amma, an kai wa ƴan sanda kara,” a cewarsa.

Wani mazaunin yankin mai suna Shehu, ya bayyana yadda mutane uku suka samu raunuka yayin aukuwar lamarin.

A cewarsa, rundunar cire bam ta isa wurin, inda ta tsaida tashin wani abu mai fashewan.

“Daga cikin mutane ukun da suka samu raunukan, akwai mai P.O.S din wanda baya cikin hayyacin shi, sannan yana samun kulawa a asibitin 44, inda sauran mutane biyu suka samu kananan raunuka,” a cewarsa.

Sai dai, gwamnatin jihar da ƴan sandan jihar har yanzu ba su yi tsokaci game da lamarin ba. Kakakin rundunar, ASP Jalige Mohammed, bai amsa kiran wayar da aka yi masa ba.

Daily Trust ta ruwaito yadda fashewar abun yazo wasu makonni bayan gwamnatin jihar ta bakin kwamishinan kula da lamurran cikin gida, Samuel Aruwan, ta ja kunnen mazauna yankin da su zama masu sa ido, saboda ƴan ta’adda na shirin dasa abubuwa masu fashewa a makarantu, kasuwanni da wuraren bauta.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp