Home Taska Rundunar ‘Yan Sandan Jahar Neja Sun Kama Mai Kai wa ‘Yan Bindiga...

Rundunar ‘Yan Sandan Jahar Neja Sun Kama Mai Kai wa ‘Yan Bindiga Abinci

'Yan Ta'adda

Rundunar ‘Yan Sandan Jahar Neja Sun Kama Mai Kai wa ‘Yan Bindiga Abinci

Rundunar ‘yan sandan Jihar Neja ta yi ram da wani Umar Dauda, mai shekaru 20 da ake zargin yana kai wa ‘yan ta’addan jihar kayan abinci.

An samu wannan bayanin ne ta wata takarda wacce kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Wasiu Abiodun ya sanya wa hannu.

A cewarsa, sun samu bayanan sirri ne a ranar 16 ga watan Maris din 2022 akan yadda ake ganin shige da ficen matashin da kayan abinci a kauyen Kapako da ke Lapai.

Neja – Rundunar ‘yan sandan Jihar Neja ta kama wani matashi mai shekaru 20, Umar Dauda wanda ake zargin yana kai wa ‘yan ta’adda kayan abinci a jihar, The Punch ta ruwaito.

A wata takarda wacce jami’in hulda da jama’an rundunar ‘yan sandan jihar, Wasiu Abiodun ya sanya wa hannu, an samu bayani akan yadda aka kama matashin bayan mazauna yankin sun bayar da bayanan sirri ga hukuma.

An samu kudi mai yawa a hannunshi

Kamar yadda takardar tazo:

“An yi kamen ne a ranar 16 ga watan Maris din 2022, da misalin karfe 11 na dare bayan samun bayanan sirri akan yadda ake yawan ganin wani mai kai wa ‘yan ta’adda kayan abinci a kauyen Kapako da ke Lapai.”

Abiodun ya ce an tura rundunar ‘yan sanda daga ofishin Lapai da wasu ‘Yan Sa Kai zuwa kauyen bayan kwashe sa’o’i ana kulawa da shige da ficensa. Daga nan suka kama shi.

Kakakin ya ce bayan bincike shi tas, an gano wasu kayan abinci da kudade a wurin shi.

The Punch ta nuna yadda ya ce:

“Bayan kama shi, an samu sinkin biredi 6, goruna 4 na wani lemu Fearless, gorunan Maltina 5, dauri 5 na wani ganye da ake zargin wiwi ne, wanke danye da shinkafa, sai kuma kudi N90,000,000.”

Ya amsa laifukansa

Ya ci gaba da shaida yadda wanda ake zargin ya amsa laifukansa na kai wa ‘yan bindiga kayan abinci, kuma suna bin shi har sansaninsa don amsar kayan abincin.

Ya kara da cewa, Dauda ya shaida cewa wannan ne karonsa na 4 na kai wa ‘yan bindigan kayan abinci kafin a kama shi.

Takardar ta ci gaba da shaida yadda aka duba gidansa inda aka ga wata bindigar toka kuma ya amsa da cewa nashi ne.

Ya ce ya siya bindigar ne a N65,000 a hannun wani mai hada bindigogi a kauyen, kuma yana ajiyeta ne don kare kansa.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp