Home Taska ‘Yan Bindiga Sun Sace Mutane 40 a Harin da Suka kai Jahar...

‘Yan Bindiga Sun Sace Mutane 40 a Harin da Suka kai Jahar Neja

'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Sace Mutane 40 a Harin da Suka kai Jahar Neja

Wasu miyagun ‘yan bindiga sun kai farmaki yankin jihar Neja, sun sace Rabaran da wasu mutane sama da 40.

Wannan na zuwa jim kadan bayan da gwamnati ta karfafi gwiwar mazauna kan komawa yankunansu.

Rahotanni sun tattaro cewa, kungiyar kiristoci ta Najeriya reshen jihar Neja ta tabbatar da faruwar lamarin.

jihar Neja – Wasu ‘yan bindiga sun kai farmaki Neja jiya Lahadi sun yi awon gaba da limamin cocin Katolika na Cocin St Mary da ke Sarkin Pawa, hedikwatar karamar hukumar Munya ta Jihar Neja, Rabaran Leo Raphael Ozigi da wasu mutanen kauyen 44.

Daily Trust ta ce ta samu labarin cewa, an yi garkuwa da Rabaran ne a hanyarsa ta zuwa Gwada daga Sarkin Pawa a lokacin da ya ci karo da ‘yan bindiga da ke barna, inda suka yi taho-mu-gama da shi tare da wasu mutanen kauyen.

Sakataren kungiyar Kiristocin Najeriya reshen jihar Neja, Fasto Raphael Opawoye, ya tabbatar da sace Rabaran Ozigi.

A cewarsa:

“An yi garkuwa da Rabaran Dr Leo Raphael Ozigi ranar Lahadi a hanyarsa ta komawa Gwada daga Sarkin Pawa bayan hidimar bautar ta ranar Lahadi.”

Sakataren karamar hukumar Munya, James Jagaba, ya bayyana sabon barnar ‘yan bindiga a karamar hukumar Munya a matsayin abin takaici.

Yace:

“Ilahirin hukumar Munya tana cikin tashin hankali. Halin da ake ciki a yankin yana da ban tsoro. Ana yin garkuwa da mutane a dukkan sassan kananan hukumomin.”

An sace wasu mutane 44 a yankin

Wani mazaunin yankin mai suna Shehu Abubakar, ya shaida wa Daily Trust cewa wasu mutanen kauyen 44 da aka sace na daga cikin wadanda suke koma yankunansu daga sansanonin ‘yan gudun hijira a ranar Asabar.

A cewarsa:

“Muna cikin damuwa saboda da alama matsalar mu ba ta kare ba. Jama’a sun fara dawowa ranar Asabar don shirin noman doya.

“Gwamnati ta karfafe mu mu koma ga yankunanmu cewa za a yi shirye-shiryen magance tsaro. A ranar Asabar ne mutane suka fara dawowa kuma wadannan miyagu sun sake farmakarmu.”

Abubakar ya koka da yadda ‘yan bindigan da ke cin karensu ba babbaka tun ranar Asabar suke barna a hanyar Sarkin Pawa zuwa Gwada tare da garken shanun da suka yi awon gaba da su a lokacin da suke kai hare-hare kan mazauna.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp