Home Taska ‘Yan Bindiga Sun Sace Mutane 40 a Harin da Suka kai Jahar...

‘Yan Bindiga Sun Sace Mutane 40 a Harin da Suka kai Jahar Neja

'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Sace Mutane 40 a Harin da Suka kai Jahar Neja

Wasu miyagun ‘yan bindiga sun kai farmaki yankin jihar Neja, sun sace Rabaran da wasu mutane sama da 40.

Wannan na zuwa jim kadan bayan da gwamnati ta karfafi gwiwar mazauna kan komawa yankunansu.

Rahotanni sun tattaro cewa, kungiyar kiristoci ta Najeriya reshen jihar Neja ta tabbatar da faruwar lamarin.

jihar Neja – Wasu ‘yan bindiga sun kai farmaki Neja jiya Lahadi sun yi awon gaba da limamin cocin Katolika na Cocin St Mary da ke Sarkin Pawa, hedikwatar karamar hukumar Munya ta Jihar Neja, Rabaran Leo Raphael Ozigi da wasu mutanen kauyen 44.

Daily Trust ta ce ta samu labarin cewa, an yi garkuwa da Rabaran ne a hanyarsa ta zuwa Gwada daga Sarkin Pawa a lokacin da ya ci karo da ‘yan bindiga da ke barna, inda suka yi taho-mu-gama da shi tare da wasu mutanen kauyen.

Sakataren kungiyar Kiristocin Najeriya reshen jihar Neja, Fasto Raphael Opawoye, ya tabbatar da sace Rabaran Ozigi.

A cewarsa:

“An yi garkuwa da Rabaran Dr Leo Raphael Ozigi ranar Lahadi a hanyarsa ta komawa Gwada daga Sarkin Pawa bayan hidimar bautar ta ranar Lahadi.”

Sakataren karamar hukumar Munya, James Jagaba, ya bayyana sabon barnar ‘yan bindiga a karamar hukumar Munya a matsayin abin takaici.

Yace:

“Ilahirin hukumar Munya tana cikin tashin hankali. Halin da ake ciki a yankin yana da ban tsoro. Ana yin garkuwa da mutane a dukkan sassan kananan hukumomin.”

An sace wasu mutane 44 a yankin

Wani mazaunin yankin mai suna Shehu Abubakar, ya shaida wa Daily Trust cewa wasu mutanen kauyen 44 da aka sace na daga cikin wadanda suke koma yankunansu daga sansanonin ‘yan gudun hijira a ranar Asabar.

A cewarsa:

“Muna cikin damuwa saboda da alama matsalar mu ba ta kare ba. Jama’a sun fara dawowa ranar Asabar don shirin noman doya.

“Gwamnati ta karfafe mu mu koma ga yankunanmu cewa za a yi shirye-shiryen magance tsaro. A ranar Asabar ne mutane suka fara dawowa kuma wadannan miyagu sun sake farmakarmu.”

Abubakar ya koka da yadda ‘yan bindigan da ke cin karensu ba babbaka tun ranar Asabar suke barna a hanyar Sarkin Pawa zuwa Gwada tare da garken shanun da suka yi awon gaba da su a lokacin da suke kai hare-hare kan mazauna.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp