Home Taska Gwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026

Gwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026

Gwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026

 

Gwamnatin Najeriya ta ƙudiri anyiar samun naira tiriliyan 2.5 na kuɗaɗen shiga na cikin gida a shekarar 2026.

Mukaddashin Shugaban Hukumar Kula da Ɗa’a a Harkokin Kasafin Kuɗi ta Ƙasa, Charles Abana ne ya bayyana hakan yayin wata ganawa tsakanin shugabannin hukumar da Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume, a Abuja.

A wata sanarwa da mai magana da yawun Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya, Chris Ugwuegbulam, ya fitar, Mista Abana ya ce an ɗauki wannan mataki ne bayan hukumar ta sa ido kan kuɗaɗen shiga na kusan naira tiriliyan 1.84 da ma’aikatun gwamnati da hukumominta suka samar zuwa watan Satumban 2025.

Ya ce, “Ta hanyar ƙara sa ido kan rarar kuɗaɗen shiga na kamfanonin gwamnati da kuma kuɗaɗen shiga da ma’aikatu da hukumomin gwamnati ke samarwa, hukumar ta lura da kuɗaɗen shiga na kusan naira tiriliyan 1.84 zuwa watan Satumban 2025, kuma yanzu ta ƙudiri aniyar samun naira tiriliyan 2.5 a matsayin kuɗaɗen shiga na shekarar 2026.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp