Home Taska Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga Legas

Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga Legas

Accident

Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga Legas

Wasu Sakkwatawa kimanin mutum 18 sun riga mu gidan gaskiya a wani mummunan hatsarin mota da ya auku a kan babbar hanyar Yauri da ke Jihar Kebbi.

Aminiya ta ruwaito cewa ƙarar kwana ta cimma mutanen ne a yayin da suke kan hanyarsu ta dawowa daga Legas, inda suka je suka shafe tsawon lokaci suna neman na kai.

Mamatan dai na cikin fasinjoji 20 da ke cikin wata motar haya mai ɗaukar mutum 18, wadda ta yi taho-mu-gama da wata babbar mota da misalin ƙarfe 11:00 na daren Litinin, inda mutum 18 suka mutu nan take, yayin da ragowar biyun suka tsira da ƙananan raunuka.

Bello Muhammad, mamba na Ƙungiyar Direbobin Motoci ta Ƙasa (NURTW), kuma abokin direban motar, ya ce shi da wasu abokan aiki ne suka garzaya wurin domin kwaso gawarwakin mamatan bayan sun samu labarin hatsarin.

Ya ce sun isa wurin da misalin ƙarfe 4:00 na asubahin ranar Talata, inda suka tarar motar hayar ta yi mummunan karo da wata babbar mota.

“An kira aka sanar da mu cewa abokin aikinmu ya yi hatsari bayan garin Yauri. Da muka isa wurin, mutum 18 sun riga sun rasu, motar kuma ta tarwatse,” in ji shi.

A cewarsa, an kai gawarwakin zuwa Babban Asibitin Yauri domin tantance su kafin a miƙa su ga iyalansu.

Ya ƙara da cewa shi ne ya tuƙa motar da ta ɗauko gawarwakin mutanen da suka fito daga Gundumar Kajiji zuwa garuruwansu domin yi musu jana’iza.

A cewarsa, mutum ɗaya ne kacal daga cikin fasinjojin ya fito daga Ƙaramar Hukumar Gwandu ta Jihar Kebbi, yayin da sauran 19 ’yan asalin Jihar Sakkwato ne.

Ya kuma ce ɗaya daga cikin mutane biyu da suka tsira shi ne yaron motar, wanda ya yi bankwana da direban kafin su bar Legas.

Muhammad ya ce daga cikin mamatan akwai direban motar, Manniru Sabo, da Basiru Shehu, dukkansu daga ƙauyen Kajiji, da kuma wani mutum daga wani ƙauye da ke ƙarƙashin gundumar.

Ya ƙara da cewa akwai kuma wasu mutum bakwai daga cikin mamatan da suka fito daga ƙauyukan Bingaje da Gudirriga na Ƙaramar Hukumar Yabo, yayin da mutum biyu suka fito daga Ƙaramar Hukumar Gada. Sauran kuma sun fito daga wasu yankuna daban-daban na Jihar Sakkwato.

Bello ya ce ana sa ran za a binne wasu daga cikin mamatan a Yauri saboda yadda gawarwakinsu suka tarwatse, yayin da aka kawo gawarwakin mutanen Kajiji gida, inda aka yi musu jana’iza bisa koyarwar addinin Musulunci.

 

Shi ma Alhaji Shehu Muslim Jabo, makusancin direban motar, ya ce ya taimaka wajen ɗauko gawarwakin zuwa Kajiji sannan ya halarci jana’izar mamatan da suka fito daga Ƙaramar Hukumar Shagari.

Ya ce lamarin ya girgiza al’umma matuƙa musamman la’akari da yadda wasu daga cikin gawarwakin suka tawarwatse ƙwarai.

“Muna cikin matsanancin alhini saboda yadda gawarwakin suka kasance. Wasu ma ba a iya gane su cikin sauƙi,” in ji shi.

Jabo ya yi zargin cewa wata babbar mota mallakin kamfanin Dangote ce ta kauce daga hanyarta ta bugi motar hayar, lamarin da ya haddasa hatsarin.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp