Home Taska An Kama Mai Taimakawa ‘Yan Kungiyar Lakurawa Wajen Samun Kudi a Jihar...

An Kama Mai Taimakawa ‘Yan Kungiyar Lakurawa Wajen Samun Kudi a Jihar Sokoto

Police-Arrest

An Kama Mai Taimakawa ‘Yan Kungiyar Lakurawa Wajen Samun Kudi a Jihar Sokoto

 

Jihar Sokoto, Nigeria – Rundunar ‘yan sandan Sokoto ta sanar da cafke wasu da ake zargi da ba ‘yan bindiga bayanai da kuma taimaka masu wajen samun kudade.

Kwamishinan ‘yan sanda na Sokoto, Hayatu Hassan Shaffa, ya ce a ranar 17 ga Afrilu, 2026, jami’an sashen yaki da garkuwa da mutane sun kama wani Aminu Mai Roba daga kauyen Maikulki da ke karamar hukumar Binji.

Jaridar Leadership ta rahoto cewa da yake hira da manema labarai, ya ce an tare wanda ake zargin ne a kan hanyar Ruwa-Wuri zuwa Tangaza dauke da shanu guda hudu.

An samu bayanai daga bakin mutumin

A cewar CP Hayatu, bincike ya nuna cewa wanda ake zargin ya amsa cewa ya karbi shanun ne daga kungiyar ‘yan ta’adda ta Lakurawa a kauyen Wariya da ke Tangaza.

“Ya bayyana cewa aikinsa shi ne sayar da shanun sannan ya mayar da kudin ga kungiyar ‘yan ta’addan. Mun fara hada hujjoji yayin da ake ci gaba da bincike kan lamarin.” in ji shi.

Kwamishinan ‘yan sandan ya ce wannan na daga cikin kokarin rundunar wajen tabbatar da gaskiya da kuma karfafa hadin gwiwa tsakanin ‘yan sanda da al’umma

Ya jaddada cewa rundunar na ci gaba da kokarin kare rayuka da dukiyoyin jama’a tare da dakile aikata laifuka, kamar yadda Daily Post ta kawo.

Jami’an tsaro sun fatattaki yan bindiga

Ya kuma bayyana cewa a ranar 8 ga Afrilu, da misalin karfe 4:20 na safe, ‘yan sanda sun samu kiran gaggawa kan harin da ‘yan bindiga suka kai kauyukan Kwarengamba da Gayya da Kwari a karamar hukumar Sabon Birni

A cewarsa, jami’an ‘yan sanda tare da sojoji, ‘yan sa-kai da masu tsaron al’umma sun kai dauki cikin gaggawa.

Ya ce hadakar jami’an tsaron ta fafata da ‘yan bindigar inda aka fatattake su bayan musayar wuta mai tsanani.

“Maharan sun tsere da raunukan harbi zuwa cikin daji, sannan suka bar buhu dauke da harsasai 167,” in ji shi.

Kwamishinan ya yaba da kokarin jami’an tsaro, yana mai cewa nasarorin da aka samu na nuna kwarewa da jarumtaka, tare da karfafa hadin gwiwa tsakanin hukumomin tsaro daban-daban da al’umma baki daya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp