Home Taska ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Dakunan Kwanan Dalibai a Jami’ar OOU

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Dakunan Kwanan Dalibai a Jami’ar OOU

OOU

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Dakunan Kwanan Dalibai a Jami’ar OOU

 

Jihar Ogun, Nigeria – Wasu ‘yan bindiga da ake zargin ‘yan fashi da makami ne sun kai hari dakunan kwanan dalibai a Jami’ar Olabisi Onabanjo (OOU) da ke Ibogun a jihar Ogun.

Rahotanni sun nuna cewa maharan sun bude wuta daga shiga cikin gidan kwanan da tsakar daren jiya Juma’a, lamarin da ya jefa dalibai cikin firgici yayin da suka rika guduwa domin tsira.

Mahara sun bude wuta a dakunan kwana Rahotan jaridar The Nation ya ce harin ya fara ne da tsakar dare, ya kuma ci gaba har zuwa safiyar Asabar, inda sama da mutane 12 dauke da makamai suka shiga dakunan kwanan dalibai da dama.

An ce maharan sun rika harbe-harbe domin tsoratar da dalibai kafin su kwashe wayoyi, kwamfutoci da sauran kayayyaki masu daraja.

Yadda daliban OOU suka shiga firgici

Wani mai amfani da kafar sada zumunta, Michael Mabayomije, ya bayyana cewa maharan sun yi aiki na tsawon lokaci ba tare da jami’an tsaro sun kai dauki ba.

Ya ce dalibai da dama sun jikkata a harin, yayin da wasu kuma suka shiga matsanancin firgici saboda tashin hankalin da suka gani.

Jaridar Punch ta kuma rawaito cewa an ga jini a bango da bene na daya daga cikin gidajen kwanan dalibai da abin ya shafa.

Mazauna Ibogun sun bayyana lamarin a matsayin mai tayar da hankali, inda suka ce karar bindiga ta karade harabar jami’ar yayin da dalibai ke kokarin tserewa domin ceton rayuwarsu

Wasu daga cikin wadanda abin ya shafa sun samu raunuka yayin da suke kokarin gudu ko kuma tsayawa kare kansu.

Wane mataki yan sanda suka dauka?

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Ogun, Oluseyi Babaseyi, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce tuni jami’ai suka kaddamar da bincike kan lamarin.

Ya ce an fara bincike kan harin, tare da tura jami’an tsaro ciki har da DPO na yankin Ibogun da kuma kwamandan da ke kula da yankin domin duba halin da ake ciki da kuma kwantar da hankalin dalibai da mazauna yankin.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp