Home Taska ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Dakunan Kwanan Dalibai a Jami’ar OOU

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Dakunan Kwanan Dalibai a Jami’ar OOU

OOU

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Dakunan Kwanan Dalibai a Jami’ar OOU

 

Jihar Ogun, Nigeria – Wasu ‘yan bindiga da ake zargin ‘yan fashi da makami ne sun kai hari dakunan kwanan dalibai a Jami’ar Olabisi Onabanjo (OOU) da ke Ibogun a jihar Ogun.

Rahotanni sun nuna cewa maharan sun bude wuta daga shiga cikin gidan kwanan da tsakar daren jiya Juma’a, lamarin da ya jefa dalibai cikin firgici yayin da suka rika guduwa domin tsira.

Mahara sun bude wuta a dakunan kwana Rahotan jaridar The Nation ya ce harin ya fara ne da tsakar dare, ya kuma ci gaba har zuwa safiyar Asabar, inda sama da mutane 12 dauke da makamai suka shiga dakunan kwanan dalibai da dama.

An ce maharan sun rika harbe-harbe domin tsoratar da dalibai kafin su kwashe wayoyi, kwamfutoci da sauran kayayyaki masu daraja.

Yadda daliban OOU suka shiga firgici

Wani mai amfani da kafar sada zumunta, Michael Mabayomije, ya bayyana cewa maharan sun yi aiki na tsawon lokaci ba tare da jami’an tsaro sun kai dauki ba.

Ya ce dalibai da dama sun jikkata a harin, yayin da wasu kuma suka shiga matsanancin firgici saboda tashin hankalin da suka gani.

Jaridar Punch ta kuma rawaito cewa an ga jini a bango da bene na daya daga cikin gidajen kwanan dalibai da abin ya shafa.

Mazauna Ibogun sun bayyana lamarin a matsayin mai tayar da hankali, inda suka ce karar bindiga ta karade harabar jami’ar yayin da dalibai ke kokarin tserewa domin ceton rayuwarsu

Wasu daga cikin wadanda abin ya shafa sun samu raunuka yayin da suke kokarin gudu ko kuma tsayawa kare kansu.

Wane mataki yan sanda suka dauka?

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Ogun, Oluseyi Babaseyi, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce tuni jami’ai suka kaddamar da bincike kan lamarin.

Ya ce an fara bincike kan harin, tare da tura jami’an tsaro ciki har da DPO na yankin Ibogun da kuma kwamandan da ke kula da yankin domin duba halin da ake ciki da kuma kwantar da hankalin dalibai da mazauna yankin.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp