Home Taska An Kama Mai Taimakawa ‘Yan Kungiyar Lakurawa Wajen Samun Kudi a Jihar...

An Kama Mai Taimakawa ‘Yan Kungiyar Lakurawa Wajen Samun Kudi a Jihar Sokoto

Police-Arrest

An Kama Mai Taimakawa ‘Yan Kungiyar Lakurawa Wajen Samun Kudi a Jihar Sokoto

 

Jihar Sokoto, Nigeria – Rundunar ‘yan sandan Sokoto ta sanar da cafke wasu da ake zargi da ba ‘yan bindiga bayanai da kuma taimaka masu wajen samun kudade.

Kwamishinan ‘yan sanda na Sokoto, Hayatu Hassan Shaffa, ya ce a ranar 17 ga Afrilu, 2026, jami’an sashen yaki da garkuwa da mutane sun kama wani Aminu Mai Roba daga kauyen Maikulki da ke karamar hukumar Binji.

Jaridar Leadership ta rahoto cewa da yake hira da manema labarai, ya ce an tare wanda ake zargin ne a kan hanyar Ruwa-Wuri zuwa Tangaza dauke da shanu guda hudu.

An samu bayanai daga bakin mutumin

A cewar CP Hayatu, bincike ya nuna cewa wanda ake zargin ya amsa cewa ya karbi shanun ne daga kungiyar ‘yan ta’adda ta Lakurawa a kauyen Wariya da ke Tangaza.

“Ya bayyana cewa aikinsa shi ne sayar da shanun sannan ya mayar da kudin ga kungiyar ‘yan ta’addan. Mun fara hada hujjoji yayin da ake ci gaba da bincike kan lamarin.” in ji shi.

Kwamishinan ‘yan sandan ya ce wannan na daga cikin kokarin rundunar wajen tabbatar da gaskiya da kuma karfafa hadin gwiwa tsakanin ‘yan sanda da al’umma

Ya jaddada cewa rundunar na ci gaba da kokarin kare rayuka da dukiyoyin jama’a tare da dakile aikata laifuka, kamar yadda Daily Post ta kawo.

Jami’an tsaro sun fatattaki yan bindiga

Ya kuma bayyana cewa a ranar 8 ga Afrilu, da misalin karfe 4:20 na safe, ‘yan sanda sun samu kiran gaggawa kan harin da ‘yan bindiga suka kai kauyukan Kwarengamba da Gayya da Kwari a karamar hukumar Sabon Birni

A cewarsa, jami’an ‘yan sanda tare da sojoji, ‘yan sa-kai da masu tsaron al’umma sun kai dauki cikin gaggawa.

Ya ce hadakar jami’an tsaron ta fafata da ‘yan bindigar inda aka fatattake su bayan musayar wuta mai tsanani.

“Maharan sun tsere da raunukan harbi zuwa cikin daji, sannan suka bar buhu dauke da harsasai 167,” in ji shi.

Kwamishinan ya yaba da kokarin jami’an tsaro, yana mai cewa nasarorin da aka samu na nuna kwarewa da jarumtaka, tare da karfafa hadin gwiwa tsakanin hukumomin tsaro daban-daban da al’umma baki daya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp