Home SIYASA 2027: Jam’iyyun Adawa Sun Sanar da Shirinsu na Yakar Tinubu da APC

2027: Jam’iyyun Adawa Sun Sanar da Shirinsu na Yakar Tinubu da APC

Atiku

2027: Jam’iyyun Adawa Sun Sanar da Shirinsu na Yakar Tinubu da APC

 

Birnin Ibadan, jihar Oyo – Jam’iyyun adawa sun sanar da shirinsu na fafatawa da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu a zaben shekarar 2027.

Jam’iyyun adawar sun bayyana shirinsu na gabatar da ɗan takarar shugaban ƙasa guda ɗaya tilo domin zaɓen shekarar 2027.

Jaridar The Cable ta kawo rahoton cewa jam’iyyun adawar sun amince da wannan matsayar ne a ranar Asabar, 25 ga watan Afirilun 2026.

‘Yan adawa sun yi taro a Ibadan

An cimma matsayar ne yayin babban taron shugabannin jam’iyyun adawa na ƙasa da aka gudanar a Ibadan, babban birnin jihar Oyo.

Jaridar Vanguard ta ce an bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da aka fitar bayan babban taron da jam’iyyun adawar suka gudanar.

Manyan jiga-jigan adawa da suka haɗa da Atiku Abubakar, Rabiu Musa Kwankwaso, Rotimi Amaechi, Peter Obi da Rauf Aregbesola, sun halarci taron.

‘Yan adawa za su yaki Tinubu da APC

Yayin da yake karanta sanarwar, shugaban wani ɓangare na jam’iyyar PDP, Taminu Turaki, ya ce bayyana cewa:

“Za mu bijire wa duk wata makirci na APC na son mayar da Najeriya ƙasa mai jam’iyya ɗaya tilo, kuma za mu yi yaƙi domin dorewar tsarin dimokuraɗiyya mai jam’iyyu da dama a ƙasarmu.”

Game da zaɓen 2027, ‘yan adawar sun yi watsi da iƙirarin cewa an riga an san sakamakon zaɓen, inda suka bayyana cewa:

“Duk da dabarun jam’iyya mai mulki, za mu fitar da ’yan takara kuma mu fafata a zaɓen shugaban ƙasa da sauran zaɓukan 2027.”

An cimma matsaya kan fitar da dan takara Jam’iyyun adawar sun kuma bayyana shirinsu na tsayawa takara a ƙarƙashin inuwa ɗaya, inda suka ce:

“Za mu yi aiki wajen fitar da ɗan takarar shugaban ƙasa guda ɗaya na zaɓen 2027, wanda dukkan jam’iyyun adawa da ke halartar taron za su amince da shi tare da ba shi goyon baya domin ceto al’ummarmu da suka daɗe suna shan wahala.”

Dangane da fargaba game da hukumar zaɓen, sanarwar ta bayyana cewa:

“Shugaban hukumar INEC, Joash Ojo Amupitan, tun da ya nuna son zuciya da nuna goyon baya ga jam’iyyar APC mai mulki, bai kamata ya gudanar da babban zaɓen 2027 ba.”

Sun soki tsare jiga-jigan ‘yan adawa Haka kuma sanarwar ta taɓo batun zargin danne haƙƙin siyasa, inda ta ce:

“Dukkan manyan ’yan siyasa da ake tsare da su ko ake muzantawa kan laifuffukan da za a iya bayar da belinsu, a sake su nan take kuma a ba su damar amfani da haƙƙinsu na ’yan ƙasa wajen shiga harkokin siyasa ba tare da nuna bambanci ba.”

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp