Home SIYASA 2027: Jam’iyyun Adawa Sun Sanar da Shirinsu na Yakar Tinubu da APC

2027: Jam’iyyun Adawa Sun Sanar da Shirinsu na Yakar Tinubu da APC

Atiku

2027: Jam’iyyun Adawa Sun Sanar da Shirinsu na Yakar Tinubu da APC

 

Birnin Ibadan, jihar Oyo – Jam’iyyun adawa sun sanar da shirinsu na fafatawa da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu a zaben shekarar 2027.

Jam’iyyun adawar sun bayyana shirinsu na gabatar da ɗan takarar shugaban ƙasa guda ɗaya tilo domin zaɓen shekarar 2027.

Jaridar The Cable ta kawo rahoton cewa jam’iyyun adawar sun amince da wannan matsayar ne a ranar Asabar, 25 ga watan Afirilun 2026.

‘Yan adawa sun yi taro a Ibadan

An cimma matsayar ne yayin babban taron shugabannin jam’iyyun adawa na ƙasa da aka gudanar a Ibadan, babban birnin jihar Oyo.

Jaridar Vanguard ta ce an bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da aka fitar bayan babban taron da jam’iyyun adawar suka gudanar.

Manyan jiga-jigan adawa da suka haɗa da Atiku Abubakar, Rabiu Musa Kwankwaso, Rotimi Amaechi, Peter Obi da Rauf Aregbesola, sun halarci taron.

‘Yan adawa za su yaki Tinubu da APC

Yayin da yake karanta sanarwar, shugaban wani ɓangare na jam’iyyar PDP, Taminu Turaki, ya ce bayyana cewa:

“Za mu bijire wa duk wata makirci na APC na son mayar da Najeriya ƙasa mai jam’iyya ɗaya tilo, kuma za mu yi yaƙi domin dorewar tsarin dimokuraɗiyya mai jam’iyyu da dama a ƙasarmu.”

Game da zaɓen 2027, ‘yan adawar sun yi watsi da iƙirarin cewa an riga an san sakamakon zaɓen, inda suka bayyana cewa:

“Duk da dabarun jam’iyya mai mulki, za mu fitar da ’yan takara kuma mu fafata a zaɓen shugaban ƙasa da sauran zaɓukan 2027.”

An cimma matsaya kan fitar da dan takara Jam’iyyun adawar sun kuma bayyana shirinsu na tsayawa takara a ƙarƙashin inuwa ɗaya, inda suka ce:

“Za mu yi aiki wajen fitar da ɗan takarar shugaban ƙasa guda ɗaya na zaɓen 2027, wanda dukkan jam’iyyun adawa da ke halartar taron za su amince da shi tare da ba shi goyon baya domin ceto al’ummarmu da suka daɗe suna shan wahala.”

Dangane da fargaba game da hukumar zaɓen, sanarwar ta bayyana cewa:

“Shugaban hukumar INEC, Joash Ojo Amupitan, tun da ya nuna son zuciya da nuna goyon baya ga jam’iyyar APC mai mulki, bai kamata ya gudanar da babban zaɓen 2027 ba.”

Sun soki tsare jiga-jigan ‘yan adawa Haka kuma sanarwar ta taɓo batun zargin danne haƙƙin siyasa, inda ta ce:

“Dukkan manyan ’yan siyasa da ake tsare da su ko ake muzantawa kan laifuffukan da za a iya bayar da belinsu, a sake su nan take kuma a ba su damar amfani da haƙƙinsu na ’yan ƙasa wajen shiga harkokin siyasa ba tare da nuna bambanci ba.”

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Cikakken Bayani Game da Kitsa Juyin Mulki a NajeriyaIdan Suna Buƙatar Tattaunawa, sa kira mu - Trump ga Iran'Yan Bindiga Sun Kai Hari Dakunan Kwanan Dalibai a Jami'ar OOUAn Kama Mai Taimakawa 'Yan Kungiyar Lakurawa Wajen Samun Kudi a Jihar Sokoto2027: Jam’iyyun Adawa Sun Sanar da Shirinsu na Yakar Tinubu da APC'Yan Siyasa ba sa yi wa Talakawan da Suke Jagoranta Adalci - Sanata NingiRahoton ‘Yan Sanda ya Danganta Kashi 70% na Laifuka a Kano da Shaye-Shayen Miyagun Ƙwayoyi, Ya Gano Mutane 513 da ake Zargin Masu Safara NePantami Ya Samu Karfin Gwiwa Yayin Da Jama'a Ke Taya Shi Murna a Lokacin Ziyarar Ayyuka a GombeMa’aikatar Tsaro ta yi Karin Bayani Kan Yarjejeniyar Yaki da Ta’addanci da Turkiyya, ta Karyata Zargin ‘Jihadi’Tinubu na Neman Amincewar Majalisar Dattawa kan Sabon Rancen $516.3mGadon Mulkin Gombe: Wa Ke Jin Tsoron Tasirin Pantami Daga Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Masu Kera Makamai ba Bisa Ka'ida ba a Filato, Sun Kama Wadanda ake Zargi da Ta'addanci a NijarShin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da Iran
X whatsapp