Home SIYASA Shugaban Amurka ya Yaba wa Shugaba Tinubu Kan Matakan da Yake ɗauka...

Shugaban Amurka ya Yaba wa Shugaba Tinubu Kan Matakan da Yake ɗauka Wajen Yaƙi da Ta’addanci

Shugaban Amurka ya Yaba wa Shugaba Tinubu Kan Matakan da Yake ɗauka Wajen Yaƙi da Ta’addanci

 

Shugaban Amurka Donald Trump ya yaba wa shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu kan abin da ya kira “ƙwazon jagorancinsa” wajen yaƙi da ta’addanci da kuma magance matsalar tsaro a Najeriya.

Fadar shugaban ƙasar ta ce, a cikin wata wasiƙa da Trump ya aike wa Tinubu, ya ce yana yaba wa shugaban Najeriyar kan ƙudurin da yake da shi na magance matsalolin da suka addabi ƙasar, musamman hare-haren da ke shafar al’ummomin Kiristoci.

Trump ya ce babban abin alfahari ne gare shi yana tare da Tinubu wajen yaƙi da ƴan ta’adda domin ƙarfafa Najeriya da bunƙasa ta.

Ya kuma bayyana cewa dangantakar Amurka da Najeriya na da matuƙar muhimmanci a wannan lokaci da rikice-rikice ke ƙaruwa a yammacin Afirka da sauran sassan duniya.

A cewarsa, ƙasashen biyu suna da buri ɗaya na yaƙi da ta’addanci ta kowane fanni, kuma yarjejeniyar haɗin gwiwar tsaro ta shekarar 2026 tsakanin Amurka da Najeriya ta samar da ingantaccen tsarin cimma wannan buri.

Trump ya ce yana alfahari da tura rundunar musamman ta sojojin Amurka domin horas da sojojin Najeriya tare da samar musu da ƙwarewa da kayan aiki da bayanan sirri da za su taimaka wajen kare ƙasar da kuma tabbatar da tsaron ‘yan ƙasa.

A cewar gwamnatin Najeriya ta hannun Bayo Onanuga, daga cikin nasarorin haɗin gwiwar da ƙasashen biyu suka ƙula akwai harin da aka kai ranar 16 ga Mayu kan maɓoyar mayaƙan ISIS a yankin Tafkin Chadi, wanda ta ce ya yi sanadin kashe babban jagoran ƙungiyar Abubakar Al-Minoki da wasu manyan kwamandojinsa.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mawallafin PRNigeria Ya Fitar Da Littafin Tarihin Rayuwarsa Akan Rigimar NIPSS Yayin Da IMPR Ta Bayyana Cigaba Mai Karfi A Tsakiyar ShekaraShugaban Amurka ya Yaba wa Shugaba Tinubu Kan Matakan da Yake ɗauka Wajen Yaƙi da Ta'addanciBinciken Gaskiya: Shin Gajimaren ne ya ɓulɓulowa ƙasa a Hanyar Abuja Zuwa Kaduna?HRW ta Zargin Hukumomin Najeriya da Rashin Adalci ga Ƴan  ƙungiyar Boko HaramHukuncin da Kotu ta Yanke wa Matashin da ya  Yunƙurin Satar Motar Yan SandaMutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto 
X whatsapp