Home Taska Sojojin Najeriya na Neman ɗaya Daga Cikin Jami’inta Ruwa a Jallo, Kan...

Sojojin Najeriya na Neman ɗaya Daga Cikin Jami’inta Ruwa a Jallo, Kan Zargin Sayar wa Ƴan bindiga Kakin Soji

Sojojin Najeriya na Neman ɗaya Daga Cikin Jami’inta Ruwa a Jallo, Kan Zargin Sayar wa Ƴan bindiga Kakin Soji

 

 

Sashen kula da kayan aiki na rundunar sojin ƙasa ta Najeriya ta ayyana neman ɗaya daga cikin jami’inta ruwa a jallo, saboda zarginsa da sayar da kakin soji ga ”ƴanta’adda da masu aikata laifuka”.

Jami’in sojin wanda kurtu ne, mai suna Mohammed Yusuf Amutu tuni ya tsare daga wurin aikinsa bayan da zargin da ake yi masa ya fito fili.

Cikin wata sanarwar da sashen kula da kayan aikin soji na rundunar sojin ya fitar, ya ce yana ƙoƙarin gano inda sojan yake domin kama shi don fuskantar ladabtarwa.

Rundunar ta jaddada matsayin na rashin lamuntar saɓa wa aiki ko rashin ɗa’a ko duk wani abu da zai janyo wa rundunar sojin ƙasar barazana.

”Duk wani jami’inmu da muka samu da laifin taimaka wa ayyukan ƴanta’adda da masu aikata laifuka ko wasu ƙungiyoyi da gwamnati ta haramta, ta hanyar sayar musu da kakin soji ko wasu kayyaki, to zai fuskanci hukunci ƙarƙashin dokokin soji da kundin tsarin mulkin ƙasa”, kamar yadda sanarwar ta yi ƙarin haske.

Sanarwar ta kuma yi kira ga mutane su taimaka wajen kai rahoton jami’in a duk inda suka ganshi.

”Muna kira ga jama’a duk inda suka ganshi su yi ƙoƙarin sanar da sojoji mafi kusa da su ko wata hukumar tsaro mafi kusa”, in ji sanarwar.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Garkuwa da Mutane: Dakarun Sojin Najeriya Sun Kama Mutane 5 a Jihar Yobe Sojojin Najeriya na Neman ɗaya Daga Cikin Jami'inta Ruwa a Jallo, Kan Zargin Sayar wa Ƴan bindiga Kakin SojiYaɗa Farfaganda da ƙiyayya Kan Gwamnati ba Zai Kawo ƙarshenta ba - MatawalleMawallafin PRNigeria Ya Fitar Da Littafin Tarihin Rayuwarsa Akan Rigimar NIPSS Yayin Da IMPR Ta Bayyana Cigaba Mai Karfi A Tsakiyar ShekaraShugaban Amurka ya Yaba wa Shugaba Tinubu Kan Matakan da Yake ɗauka Wajen Yaƙi da Ta'addanciBinciken Gaskiya: Shin Gajimaren ne ya ɓulɓulowa ƙasa a Hanyar Abuja Zuwa Kaduna?HRW ta Zargin Hukumomin Najeriya da Rashin Adalci ga Ƴan  ƙungiyar Boko HaramHukuncin da Kotu ta Yanke wa Matashin da ya  Yunƙurin Satar Motar Yan SandaMutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar Tsaro
X whatsapp