Home Taska Jami’an Tsaro Sun Kuɓutar da Mutane 32 Yayin da 4 Suka Mutu...

Jami’an Tsaro Sun Kuɓutar da Mutane 32 Yayin da 4 Suka Mutu a Jihar Sokoto 

Jami’an Tsaro Sun Kuɓutar da Mutane 32 Yayin da 4 Suka Mutu a Jihar Sokoto 

 

Rundunar ƴansandan jihar Sokoto ta sanar da cewa mutum huɗu sun mutu bayan da wasu ’yanbindiga suka kai hari a ƙauyen Maikujera da ke ƙaramar hukumar Rabah a jihar Sokoto.

Rundunar ta ce maharan sun kutsa yankin ne suna harbe-harbe tare da yin garkuwa da mutane da kuma satar dabbobi kafin jami’an tsaro su isa wurin.

A cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar, ta ce jami’anta tare da haɗin gwiwar dakarun soji sun bazama yankin bayan samun kiran gaggawa cewa ’yanbindiga suna wucewa da shanu da suka sace tare da mutane da suka yi garkuwa da su inda suka toshe hanyoyin da ake zargin ’yan bindigar za su bi wajen tserewa.

Hakan ya janyo musayar wuta mai tsanani tsakanin jami’an tsaro da maharan, lamarin da ya tilasta wa ’yan bindigar tserewa cikin daji tare da barin mutanen da suka yi garkuwa da su da kuma dabbobin da suka sace.

Rundunar ta ce ta samu nasarar kuɓutar da mutum 32 da aka yi garkuwa da su ba tare da sun ji rauni ba.

Waɗanda aka ceto sun haɗa da maza shida da mata 26, yawancinsu yara ne.

Kwamishinan ƴansandan jihar, Hayatu Hassan Shaffa, ya miƙa sakon ta’aziyyarsa ga iyalan waɗanda suka mutu tare da jaddada cewa jami’an tsaro na ci gaba da farautar ’yan bindigar domin gurfanar da su a gaban kuliya.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Ƴan Sandan Legas Sun Kama Mutum 4 da Ake Zargi da Fashin Daji, Sun Kwato Wayoyin Hannu 25, Kwamfutoci da Kayan Ado na ZinareRundunar Sojin Ruwa Ta Rusa Wuraren Tace Mai Ba bisa Ka’ida Ba, Ta Kwato Lita 350 na AGO a Rivers2027: Yahaya Bello Ya Tara Masu Daidaita Ayyuka na A4A a Arewa ta Tsakiya Domin sake Zaban TinubuSojoji Sun Kama Mutum 2 da ake Zargi da Taimakawa Ƴan Ta’adda, Sun Kwace Kayayyakin Babur a YobePDP Ta Yi Gargadi Kan Zargin Tattara Katunan Zabe PVC da Bayanan Asusun Banki a GombeRundunar Sojojin Najeriya ta Sauya Manyan Janarori Zuwa Muhimman Mukamai na Aiki da DabaruHukumar INEC za ta ƙaddamar da Na’urar Bibiyar shirye-shiryen Zaɓen 2027 kai TsayeDaliban Tallafin Horarwa na Prnigeria Sun Ziyarci Emirate FM, Sun Samu Kyawawan Bayani Kan Watsa Labarai na DijitalNSCIA ta yi Allah Wadai da Nuna Bambancin Addini a Ci gaba da Tsare El-RufaiSarkin Ilorin Ya Yaba da Tallafin Horarwa na PRNigeria Wajen Shirya Masu Watsa Labarai na Nan GabaNDLEA Ta Kama Mai Safarar Hodar Iblis da ake Zargi da Laifi Akan Jigilar Kaya a Saudiyya, ta Kuma Kama Kwayoyi Masu Yaduwa Sama Da Miliyan 2Gwamnatin Tarayya ta Yaba da N5.41 Trillion da Kwastam ta Tara, Ta Nemi a bi Ka'idojin Duniya Hukumar Kwastam Ta Naɗa DCG, ACG 5, ta yi Nazarin Yadda aka Samu Kuɗin Shiga2027: HURIWA Ta Bukaci Ƴan Sanda da su Gurfanar da Ƴan Siyasa Kan Zargin Kalamai Masu Tada HankaliSojoji Sun Tarwatsa Maboyar Ƴan Ta'adda, Sun Kwace Bindigogin AK-47 a Sokoto 
X whatsapp