Mutane 15 Sun Mutu a Sabon Harin Yan Bindiga a Jihar Benue
Makurdi, Benue – Aƙalla mutum 15 ne aka ruwaito sun mutu a safiyar ranar Talata, 28 ga watan Yulin 2026 a wani harin ‘yan bindiga a jihar Benue.
‘Yan bindigan ɗauke da makamai sun kai sabon harin kan kauyukan Ugboju da ke ƙaramar hukumar Otukpo a jihar Benue.
Mazauna yankin sun shaida wa jaridar Daily Trust cewa harin da aka kai ƙauyen Efeyi-Ugboju ya fara ne da misalin ƙarfe 5:00 na safe a ranar Talata.
Sun bayyana cewa an gano gawarwaki 14 zuwa lokacin da ake tattara wannan rahoto.
Sun kuma ce an kashe mutum ɗaya a ƙauyen Ipom-Ugboju tun da safiyar ranar Litinin, 27 ga watan Yulin 2026.
Ana ci gaba da gano gawarwaki Mazauna yankin sun bayyana cewa adadin waɗanda suka mutu na iya ƙaruwa, domin har zuwa misalin ƙarfe 11:30 na safe ana ci gaba da gano gawarwaki.
Sun ƙara da cewa an garzaya da mutane da dama da suka samu raunuka daban-daban zuwa asibiti domin samun kulawa.
Wani mazaunin yankin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana lamarin a matsayin abin tausayi.
Read Also:
“Harin ya fara ne da misalin ƙarfe 5:00 na safe kuma ya ci gaba har bayan ƙarfe 9:00. An kashe mutum 14 a Efeyi-Ugboju, sannan waɗanda ake zargi makiyaya ne masu ɗauke da makamai sun kashe wani mutum a Ipom-Ugboju tun safiyar Litinin.” In ji shi
Shugaban ƙaramar hukuma ya tabbatar da harin
Shugaban ƙaramar hukumar Otukpo, Maxwell Ogiri, ya tabbatar da aukuwar harin yayin da yake zantawa da manema labarai a Makurdi.
Ya ce an gano gawarwaki 14 daga Efeyi-Ugboju, yayin da wasu da dama suka samu raunuka. Ogiri ya yi Allah wadai da kisan, yana mai cewa an kai harin ba tare da wata tsokana ba, kuma manufarsa ita ce kashe rayukan mutane marasa laifi.
“Babu wata tsokana. Sun zo ne kawai domin zubar da jini da kashe mutanenmu. An gano gawarwaki 14, yayin da wasu da dama suka samu raunuka.” “Mutane na rayuwa cikin tsoro, kuma akwai fargaba sosai. Mazauna maƙwabtan al’ummomi ma sun fara tserewa domin neman mafaka.” In ji shi
An nuna damuwa kan rashin tsaro
Shugaban ƙaramar hukumar ya nuna damuwa cewa duk da kasancewar jami’an tsaro, ciki har da sojoji, ‘yan sanda, rundunar MOPOL da Agro-Rangers, hare-haren na ci gaba da faruwa.
“Ban sani ba ko jami’an tsaron da ke wurin ba su isa ba. Ya kamata gwamnati ta ɗauki mataki na musamman wajen tabbatar da aiwatar da dokar hana kiwo a fili, domin komai yana da alaƙa da wannan.” In ji shi.
A nata ɓangaren, jami’ar hulɗa da jama’a ta rundunar ‘yan sandan jihar Benue (PPRO), DSP Udeme Edet, ta ce har zuwa lokacin ba ta samu cikakken bayani game da harin ba.












