Home Taska Ana Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14

Ana Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14

Ana Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14

 

Ana zargin mayaƙan Boko Haram da kashe sojojin Nijar 14 tare da jikkata wasu da dama a garin N’Guigmi da ke yankin Diffa a kudu maso gabashin ƙasar, kamar yadda shafin Actu Niger mai zaman kansa ya ruwaito.

Rahoton ya ce, bisa bayanan da aka samu daga mazauna yankin, maharan ɗauke da manyan makamai sun kai hari ne da misalin ƙarfe 9:00 na safe a ranar 31 ga Yuli, inda suka farmaki sansanin jami’an tsaro da ke wajen garin N’Guigmi a yankin Diffa.

An binne sojojin da aka kashe a wannan rana da yamma, a wani taro da Gwamnan Diffa, Manjo Janar Mahamadou Ibrahim Bagadoma, ya halarta, inda ya isar da saƙon ta’aziyyar manyan shugabannin Nijar ga iyalan mamatan tare da ƙarfafa gwiwar sojojin da ke bakin aiki.

Rahoton ya ƙara da cewa harin ya jawo martani mai ƙarfi daga dakarun Nijar, waɗanda suka ƙaddamar da farmakin ramuwar gayya domin daƙile maharan.

Sojojin sun ce sun kashe wasu daga cikin maharan, sannan suka fara wani samame da sintiri domin bibiyar sauran waɗanda suka tsere a yankin Tafkin Chadi, inda suka ce sun daɗe suna haddasa tashe-tashen hankula.

Yankin Diffa, wanda ke iyaka da Chadi a gabas da Najeriya a kudu, ya kasance ɗaya daga cikin wuraren da suka fi fama da hare-haren Boko Haram tun bayan da rikicin ya bazu zuwa Nijar a shekarar 2015.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga PantamiGazawar Demarketing: Yadda Sukar Rarara Mai Cike da Kiyayya ga Pantami Ya Rushe Daga Yushau A. ShuaibƘungiyar NARD ta yi Barazanar Shiga Yajin AikiDakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Ƴan Bindiga 3 Sun Ceto Mutane 9 da akai Garkuwa da suƳan Bindiga sun kai Hari a Kotun Shari'a da ke Jihar KatsinaBa ma Goyon Bayan a Riƙa Tura Sojoji Domin Aikin Tsaro a Lokacin Zaɓe - INECJam'iyyar NDC ta Buƙaci Sanata Hanga da Gaya da su Sake Tunani Kan Sauya SheƙaYan Bindiga Sun Kashe Kanal Abdussalam Ude Sun Raunata MatarsaMutane 15 Sun Mutu a Sabon Harin Yan Bindiga a Jihar Benue Zaɓen 2027: Uba Sani ya zaɓi MataimakinsaJami'an Tsaro Sun Kuɓutar da Mutane 32 Yayin da 4 Suka Mutu a Jihar Sokoto China ba za ta Bayar ko ta Sayar wa Iran Makamai ba a Kowane h Hali - TrumpBai Dace Obasanjo ya Danganta Marigayi Ghali Na'abba da Zargin Cin Hanci ba - AtikuGarkuwa da Mutane: Dakarun Sojin Najeriya Sun Kama Mutane 5 a Jihar Yobe Sojojin Najeriya na Neman ɗaya Daga Cikin Jami'inta Ruwa a Jallo, Kan Zargin Sayar wa Ƴan bindiga Kakin Soji
X whatsapp