Home SIYASA Yankin da Magajin Shugaba Buhari Zai Fito a 2023 – Gwamna El-Rufa’i

Yankin da Magajin Shugaba Buhari Zai Fito a 2023 – Gwamna El-Rufa’i

Yankin da Magajin Shugaba Buhari Zai Fito a 2023 – Gwamna El-Rufa’i

Gwamnan Kaduna, Malam El-Rufai ya ce APC na tsammanin ɗan takarar da zata tsayar ya fito daga kudancin kasar nan.

Gwamnan ya ce duba da kai kujerar shugaban jam’iyya arewa, suna tsammanin ɗan kudu ne zai gaji shugaba Buhari a 2023.

El-Rufai ya kuma zare kansa da maganar neman takara, amma ya ce idan Buhari ya nemi ya yi, to ba zai ƙi ba.

Abuja- Ana tsammanin ɗan takarar shugaban ƙasa a babban zaɓen 2023 dake tafe ƙarƙashin jam’iyyar APC zai fito ne daga yankin kudancin Najeriya.

Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufa’i ne ya yi wannan furucin ranar Laraba, yayin wata fira da Channels Tv.

Gwamnan ya yi bayanin cewa shugaban jam’iyyar APC na ƙasa zai fito daga Arewacin Najeriya, dan haka suke tsammanin magajin Buhari ya fito daga kudu.

A kalamansa, El-Ruafa’i ya ce:

“Muna tsammanin cewa ɗan takarar shugaban ƙasa a 2023 zai fito ne daga wani wuri a yankin kudancin Najeriya.”

A cewar Malam Nasiru, ƙusoshin jam’iyyar APC a kudu ne zasu zauna su ga wane ɓangare daga yankinsu za su baiwa takarar.

Tsohon ministan babban birnin tarayya Abuja ya ƙara da cewa, “Wuka da nama na hannun jiga-jigan APC na kudu su zakulo mana nagartaccen ɗan takara da za’a amince da shi.”

Shin APC zata iya kai bantenta a 2023?

Gwamna El-Rufa’i ya nuna kwarin guiwarsa da cewa APC zata cigaba da rike kujera lamba ɗaya a Najeriya, inda ya yi ikirarin cewa jam’iyyar na da duk abin da ake bukata na cigaba da mulki.

“Ina da yakinin a zaben 2023, APC zata lashe zaben shugaban ƙasa da kuma adadi mai yawa na kujerun gwamnoni.”

Gwamnan ya kuma zare kansa wajen shiga takarar wata kujera a zaɓe mai zuwa, amma yace zai iya fitowa takara matukar shugaba Buhari ya umarce shi da yin haka.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp