Home Taska Yanzu Haka Najeriya na da Lita 1.9bn na Man Fetur a Ajiye...

Yanzu Haka Najeriya na da Lita 1.9bn na Man Fetur a Ajiye – Mista Timipre Sylva

Yanzu Haka Najeriya na da Lita 1.9bn na Man Fetur a Ajiye – Mista Timipre Sylva

Yanzu haka Najeriya tana da lita biliyan 1.9 na man fetur a cewar karamin ministan albarkatun man fetur na Najeriya, Mista Timipre Sylva.

Ministan ya yi ikirarin cewa lita biliyan 1.9 na man fetur na iya gamzar da kasar na tsawon kwanaki 32.

Sylva ya bayyana haka ne a Abuja yayin da yake magana a gaban majalisar zartarwa ta tarayya a zaman da mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo ya jagoranta.

Timipre Sylva, Karamin Ministan Albarkatun Man Fetur ya bayyana cewa yanzu haka Najeriya na da lita biliyan 1.9 na man fetur a ajiye.

A cewarsa, wannan mai na iya gamsar da bukatun kasar na tsawon kwanaki 32, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Ministan ya bayyana haka ne jiya Laraba 9 ga watan Maris a Abuja yayin da yake magana a gaban majalisar zartarwa ta tarayya a zaman da mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo ya jagoranta.

Babban Manajin Darakta na Kamfanin Mai na Najeriya Mista Mele Kyari ya raka shi a taron na FEC da aka yi.

Babban mataimaki na musamman ga shugaban kasa, ofishin mataimakin shugaban kasa, Mista Laolu Akande ne ya bayyana haka bayan taron.

Vanguard ta Akande yana cewa:

“Akwai lodin sa’o’i 24 da ke gudana a dukkan gidajen man da ke aiki tare da Hukumar Ma’aikatar Jiha da kuma Kungiyar Dillalan Man Fetur ta Najeriya don tabbatar da cewa lamarin ya daidaita yadda ya kamata.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp