Home Taska Rikicin Rasha da Ukraine: Kasar Burtaniya ta Daskarar da Kadarorin Mai Kungiyar...

Rikicin Rasha da Ukraine: Kasar Burtaniya ta Daskarar da Kadarorin Mai Kungiyar Kwallon Kafa ta Chelsea Roman Abramovich

Rikicin Rasha da Ukraine: Kasar Burtaniya ta Daskarar da Kadarorin Mai Kungiyar Kwallon Kafa ta Chelsea Roman Abramovich

Yayin da kasashen duniya ke ci gaba da kakaba takunkumi kan gwamnatin Putin da magoya bayansa, Burtaniya ta sake daukar mataki.

Ta sanya takunkumi kan mamallakin kungiyar kwallon kafa ta Chelsea tare da bayyana shi a matsayin dan tsagin Putin.

Wannan na zuwa ne lokacin da kasar Ukraine ke ci gaba da fuskantar hare-haren bama-bamai daga kasar Rasha.

Kasar Burtaniya ta daskarar da kadarorin mai kungiyar kwallon kafa ta Chelsea Roman Abramovich, kana ta sanya haramcin mu’amala da daidaikun mutane da ‘yan kasuwa na Burtaniya, da dokar hana zirga-zirga duk dai akansa.

Sky Sports ta rahoto Firayim Ministan Burtaniya, Boris Johnson yana cewa:

“Ba zai yiwu a samar da mafaka ga wadanda suka goyi bayan mummunan harin da Putin ya kai wa Ukraine ba.”

Hakazalika, ya kara da cewa:

“Takunkumin na yau shine mataki na baya-bayan nan na goyon bayan da Birtaniya ke baiwa al’ummar Ukraine ba tare da kakkautawa ba.

“Ba za mu sassauta ba wajen kuntatawa wadanda suka taimaka wajen kashe fararen hula, lalata asibitoci da kuma mamaye wasu ‘yan uwa ba bisa ka’ida ba.

Har ila yau, sakatariyar harkokin wajen Burtaniya Liz Truss ta ce:

“Takunkumin na yau ya sake nuna cewa ‘yan kama karya da masu cika aljihu da kudin kasa ba su da wani matsayi a cikin tattalin arzikinmu ko kuma al’ummarmu. Kusancinsu da Putin ke nuna suna da hannu wajen ta’addancin nasa.

“Jinin al’ummar Ukraine na hannunsu, ya kamata su rataye kawunansu saboda kunya.

“Goyon bayanmu ga Ukraine ba zai kassara ba. Ba za mu tsaya wata-wata ba a wannan aiki na kara matsi kan gwamnatin Putin da kuma kassara kudaden na’urar yakinsa na zalunci ba.

Karin bayani na nan tafe…

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp