Home Taska ‘Yan Bindiga sun Kashe Fasto da Iyalansa a Jihar Plateau

‘Yan Bindiga sun Kashe Fasto da Iyalansa a Jihar Plateau

'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga sun Kashe Fasto da Iyalansa a Jihar Plateau

 

Jihar Plateau – ‘Yan bindiga dauke da makamai sun kai hari a ƙauyen Gako da ke ƙaramar hukumar Riyom ta jihar Plateau.

‘Yan bindigan sun kashe wani fasto da wasu daga cikin iyalinsa guda uku a yayin harin da suka kai a cikin dare.

Jaridar Daily Trust ta kawo rahoton cewa mummunan lamarin ya faru ne a ranar Lahadi, 26 ga watan Afirilun 2027.

‘Yan bindiga sun kashe fasto da iyalansa

Waɗanda abin ya shafa an bayyana sunayensu kamar haka, Fasto Ayuba Choji, matarsa Chundung Ayuba, da kuma yayansu biyu, Cyril Ayuba da Endurance Ayuba.

Maharan sun far wa ƙauyen ne da misalin ƙarfe 11:00 na dare, inda suka harbi ba kakkautawa.

Wata mazauniyar yankin, Martha Dalyop, ta shaida wa manema labarai cewa ƙarar harbin bindigar ya tursasa wa mazauna garin gudu don tsira da rayukansu.

Mutane na barin gidajensu a Plateau

Ta yi kukan cewa hare-haren da ake yawan kai wa sun ci gaba da jefa al’ummomi cikin tsoro, har ta kai da da yawa ba sa iya kwana a gidajensu ko kula da gonakinsu.

Jaridar The Punch ta ce yayin da yake tabbatar da faruwar lamarin, Sakataren yaɗa labarai na ƙungiyar matasan Berom, Rwang Tengwong, ya siffanta lamarin a matsayin abin ban tsoro.

“Wannan hari na baya-bayan nan ya nuna cewa maharan yanzu suna kai hari ne a wuraren shaƙatawa, yankunan manoma, da kuma jami’an tsaro na ‘yan sa-kai da ke kare karkara.”

– Rwang Tengwong

‘Yan bindiga sun rarrabu yayin harin Ya yi zargin cewa maharan sun rarraba kansu gida-gida ne yayin gudanar da aikin, inda wasu suka kai hari kan mazauna gari, wasu suna lalata gonaki, yayin da wani rukunin ke yin sintiri ko tare hanyoyi don hana mutane tserewa ko samun taimako. ]

Haka kuma, Tengwong ya bayyana cewa maharan sun lalata gonakin kabeji, barkono, da masara da dama a garin Kassa da ke ƙaramar hukumar Barkin Ladi a cikin sa’o’i 48 da suka gabata.

Wannan sabon lamari ya ƙara ruruta wutar fargaba a faɗin Riyom da maƙwabciyarta Barkin Ladi, inda mazauna yankin ke kiran hukumomin tsaro da na gwamnati da su tsananta ƙoƙari don dakatar da kashe-kashe da lalata hanyoyin samun abinci a jihar.

Me hukumomi suka ce kan lamarin?

Kakakin rundunar Operation Enduring Peace, Kyaftin Polycarp Oteh, da na rundunar ’yan sandan jihar Plateau, SP Alabo Alfred, ba su amsa saƙon da aka aika musu ta WhatsApp ba har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.

Al’ummar Berom sun sha zargin Fulani makiyaya da alhakin kai waɗannan hare-haren, amma shugaban ƙungiyar MACBAN na jihar, Ibrahim Yusuf Babayo, ya sha musanta waɗannan zarge-zargen, yana mai dagewa cewa mambobinsa ba su da hannu a hare-haren da ake kai musu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp