Home Taska An Ceto Marayu 15 Daga Hannun ƴan Bindiga a Jihar Kogi

An Ceto Marayu 15 Daga Hannun ƴan Bindiga a Jihar Kogi

Dahallukitab

An Ceto Marayu 15 Daga Hannun ƴan Bindiga a Jihar Kogi

 

Wasu ƴan bindiga sun sace yara 23 da mai ɗakin shugaban makaranta da gidan marayu na Dahallukitab da ke Zariagi, wani ƙauye da ke Kabba a kan titin Lokoja zuwa Okene da ke ƙaramar hukumar Adavi a jihar Kogi.

A cikin wata sanarwa da kwamishinan yaɗa labarai na jihar Kingsley Fanwo ya fitar a yau Litinin, ya ce an sace yaran ne a daren ranar jiya Lahadi.

Ya kuma ce jin kaɗan bayan samun rahoton harin, ƴan sanda tare da goyon bayan wasu jam’ain tsaro suka isa yankin, inda suka yi nasarar ceto yara 15.

Gwamnatin jihar na Allah-wadai da harin, inda ta bayar da tabbacin cewa jami’an tsaro na ci gaba da aiki wajen ceto sauran mutanen.

Sai dai sanarwar ta bayyana cewa makarantar wadda kuma take aiki a matsayin gidan marayu ba ta da rajista, inda ya ce irin waɗannan makarantu da ke irin waɗannan yankunan kuma gwamnati ba ta san da su ba, na kasancewa cikin barazana musamman a wannan lokaci na rashin tsaro.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
'Yan Daba Sun Farmaki Kasuwar Sayar da Wayoyin Hannu a Jihar KanoFarfesoshi Adamu da Pate: Manyan Gwarzayen Ilimin Sadarwa Masu Taimako Daga Yushau A. ShuaibKotu: Shuaib ya ƙi Buƙatar NIPSS na Shirin Kwace Makullin Ɗakinsa a Shari’ar SEC 47Binciken Gaskiya: Shin Faɗan Oba Femi da Brock Lesnar a Wrestlemania Gaskiya ne ?An Ceto Marayu 15 Daga Hannun ƴan Bindiga a Jihar Kogi'Yan Bindiga sun Kashe Fasto da Iyalansa a Jihar PlateauCikakken Bayani Game da Kitsa Juyin Mulki a NajeriyaIdan Suna Buƙatar Tattaunawa, sa kira mu - Trump ga Iran'Yan Bindiga Sun Kai Hari Dakunan Kwanan Dalibai a Jami'ar OOUAn Kama Mai Taimakawa 'Yan Kungiyar Lakurawa Wajen Samun Kudi a Jihar Sokoto2027: Jam’iyyun Adawa Sun Sanar da Shirinsu na Yakar Tinubu da APC'Yan Siyasa ba sa yi wa Talakawan da Suke Jagoranta Adalci - Sanata NingiRahoton ‘Yan Sanda ya Danganta Kashi 70% na Laifuka a Kano da Shaye-Shayen Miyagun Ƙwayoyi, Ya Gano Mutane 513 da ake Zargin Masu Safara NePantami Ya Samu Karfin Gwiwa Yayin Da Jama'a Ke Taya Shi Murna a Lokacin Ziyarar Ayyuka a GombeMa’aikatar Tsaro ta yi Karin Bayani Kan Yarjejeniyar Yaki da Ta’addanci da Turkiyya, ta Karyata Zargin ‘Jihadi’
X whatsapp