Home Taska Dakarun Sojin Najeriya Sun kashe ƙasurguman ’Yan Bindiga Biyu a Zamfara

Dakarun Sojin Najeriya Sun kashe ƙasurguman ’Yan Bindiga Biyu a Zamfara

Zamfara

Dakarun Sojin Najeriya Sun kashe ƙasurguman ’Yan Bindiga Biyu a Zamfara

 

Dakarun rundunar Operation Fansan Yamma na sojin Najeriya sun kashe ƙasurguman ‘yan bindiga biyu tare da wasu mayaƙa bakwai a jerin hare-haren da suka gudana cikin kwanaki uku a jihohin Zamfara da Katsina.

Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Mataimakin Daraktan Hulɗa da Jama’a na rundunar sojin, Laftanar Kanal Olaniyi Osoba, ya fitar.

Sanarwar ta ce a Jihar Zamfara, dakarun sansanin Bagega sun kai wani samame a Ƙaramar Hukumar Anka, inda suka kashe ‘yan ta’adda bakwai ciki har da manyan jagororinsu, Gomina da kuma Anaruwa, wanda ƙanin kwamandan ‘yan bindiga, Kachalla Idi Aiki.

A cewar Osoba, dakarun sun fara arangama da ‘yan ta’addan ne a kan hanyar Bagega zuwa Anka, lamarin da ya tilasta ’yan bindigar tserewa suka bar baburansa.

Sai dai daga bisani ‘yan ta’addan sun sake dawowa sansanin sojin domin daukar fansa, sai dai dakarun tare da haɗin gwiwar sojin sama sun fatattaki maharan, inda har aka samu nasarar kashe wasu uku daga ciki.

Bayanai sun ce dakarun sun ƙwato bindigogi kirar AK-47 guda biyu tare da harsasai da kuma babura bakwai.

A wani samamen da aka kai ranar 3 ga Mayu, dakarun sun sake hallaka wasu ‘yan ta’adda biyu a yankin, sai dai wani soja ya rasa ransa a filin daga.

Haka kuma, a Jihar Katsina, dakarun sansanin Fudma sun kashe ‘yan ta’adda tara ciki har da kwamandoji biyu a wata arangama da suka yi da su a kan hanyar Turare zuwa Yantumaki a Ƙaramar Hukumar Dutsinma.

Sanarwar ta ƙara da cewa an ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 guda huɗu da babura tara daga hannun ‘yan ta’addan a jihohin biyu.

Bugu da ƙari, dakarun sun kashe wasu huɗu tare da ƙwato bindigogi biyu, harsasai, wayoyin salula bakwai da kuma kuɗi Naira dubu 153.

Rundunar ta jaddada aniyarta ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin al’umma, tare da kira ga jama’a da su ci gaba da bayar da sahihan bayanai ga hukumomin tsaro domin daƙile ayyukan ta’addanci.

 

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Meyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu MohammedJami'an Tsaro Sun Kai Farmaki Sansanin IPOB/ESN, Sun Kawar da 'Yan Ta'adda 6 a AnambraOperation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Lalata Motocin Yaƙi Guda Biyu na ISWAP, Sannan Ya Kawar da Ƴan Ta'adda da Dama a BornoMai fafutuka Mahdi Shehu ya yi Gargadin Cewa Kudirin Dokar NGO Zai iya Shafar Masallatai, Coci, da Ƙungiyoyin ɗalibaiRikicin Karkashin Mulkin APC a Katsina: ADC na Radda da CSO Har Yanzu Suna Tsare a Hannun Masu ba Tinubu Shawara, MasariAnambara: Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'addan IPOB/ESN, Sun Kwato MakamaiHukumar Kwastam ta Kano ta Mika Magungunan da ba a yi wa Rijista ba ga NAFDAC, ta Kuma yi Alƙawarin Tsaurara Matakan Aiki.Operation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Kawar da 'Yan Ta'adda 36 a BornoFamadewa, Ribadu da Shirin Tsaron Kwanaki 90: Yadda YAShuaib ya Binciki Sanarwar OnanugaLabarin NIPSS Ya Bayyana Cin Zarafin Babban Jami'in Sojan Ruwa, Rear Admiral AA MustaphaƊaliban PRNigeria Sun Yaba da Gyare-Gyaren FRSC, Sun Nemi Ƙarin Ƙarfafa Sadarwa Kan Tsaron Hanya
X whatsapp