Home Taska Jami’an Tsaro sun Kashe Manyan Jagororin ’Yan Ta’adda a Katsina

Jami’an Tsaro sun Kashe Manyan Jagororin ’Yan Ta’adda a Katsina

Sojoji

Jami’an Tsaro sun Kashe Manyan Jagororin ’Yan Ta’adda a Katsina

 

Gwamnatin Jihar Katsina ta bayyana nasarar da jami’an tsaro suka samu a fafutukar da ake yi kan ’yan ta’adda, bayan da sojoji suka hallaka manyan kwamandojin ’yan ta’adda hudu a yayin sintirin yaki a kan hanyar Turare zuwa Yantumaki.

A safiyar Juma’a ne ’yan ta’adda suka gamu da ajalinsu bayan da suka kai wa sojojin hari.

Ma’aikatar Tsaron Cikin Gida da Harkokin Cikin Gida ta Jihar Katsina ta ce sojojin sun mayar da martani cikin gaggawa, suka fatattake su, suka kuma hallaka duka hudu ba tare da an samu asarar rai daga bangaren sojojin ba.

An kwato bindiga kirar AK-47 mai cike da harsasai biyar, babura guda biyu, wayoyin hannu da kuma tsabar kudi Naira N153,400 a hannunsu.

Tabbayyana cewa wasu daga cikin wayoyin da aka kwato na dauke da hotunan mutanen cikin kayan sojoji, kuma an mika su don bincike.

Binciken farko ya gano sunayen wadanda aka hallaka da suka hada da Bishir Holami, Jamilu Baki, Ibrahim Doro, da Abdurraman Maje.

Gwamnati ta bayyana su a matsayin manyan kwamandoji da ke da hannu a hare-haren da suka addabi al’ummomin Gobirawa, Raddawa, Kuki da sauran kauyuka a Dutsinma da Matazu.

Gwamnatin ta bayyana kashe su a matsayin babban cikas ga shahararren shugaban ’yan ta’adda, Muhammadu Fulani, wanda ake danganta da hare-haren ta’addanci a yankunan Matazu, Musawa, Charanchi da Kankia.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp