Home Taska Jami’an Tsaro sun Kashe Manyan Jagororin ’Yan Ta’adda a Katsina

Jami’an Tsaro sun Kashe Manyan Jagororin ’Yan Ta’adda a Katsina

Sojoji

Jami’an Tsaro sun Kashe Manyan Jagororin ’Yan Ta’adda a Katsina

 

Gwamnatin Jihar Katsina ta bayyana nasarar da jami’an tsaro suka samu a fafutukar da ake yi kan ’yan ta’adda, bayan da sojoji suka hallaka manyan kwamandojin ’yan ta’adda hudu a yayin sintirin yaki a kan hanyar Turare zuwa Yantumaki.

A safiyar Juma’a ne ’yan ta’adda suka gamu da ajalinsu bayan da suka kai wa sojojin hari.

Ma’aikatar Tsaron Cikin Gida da Harkokin Cikin Gida ta Jihar Katsina ta ce sojojin sun mayar da martani cikin gaggawa, suka fatattake su, suka kuma hallaka duka hudu ba tare da an samu asarar rai daga bangaren sojojin ba.

An kwato bindiga kirar AK-47 mai cike da harsasai biyar, babura guda biyu, wayoyin hannu da kuma tsabar kudi Naira N153,400 a hannunsu.

Tabbayyana cewa wasu daga cikin wayoyin da aka kwato na dauke da hotunan mutanen cikin kayan sojoji, kuma an mika su don bincike.

Binciken farko ya gano sunayen wadanda aka hallaka da suka hada da Bishir Holami, Jamilu Baki, Ibrahim Doro, da Abdurraman Maje.

Gwamnati ta bayyana su a matsayin manyan kwamandoji da ke da hannu a hare-haren da suka addabi al’ummomin Gobirawa, Raddawa, Kuki da sauran kauyuka a Dutsinma da Matazu.

Gwamnatin ta bayyana kashe su a matsayin babban cikas ga shahararren shugaban ’yan ta’adda, Muhammadu Fulani, wanda ake danganta da hare-haren ta’addanci a yankunan Matazu, Musawa, Charanchi da Kankia.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp