Home Taska Jami’an Tsaro sun Kashe Manyan Jagororin ’Yan Ta’adda a Katsina

Jami’an Tsaro sun Kashe Manyan Jagororin ’Yan Ta’adda a Katsina

Sojoji

Jami’an Tsaro sun Kashe Manyan Jagororin ’Yan Ta’adda a Katsina

 

Gwamnatin Jihar Katsina ta bayyana nasarar da jami’an tsaro suka samu a fafutukar da ake yi kan ’yan ta’adda, bayan da sojoji suka hallaka manyan kwamandojin ’yan ta’adda hudu a yayin sintirin yaki a kan hanyar Turare zuwa Yantumaki.

A safiyar Juma’a ne ’yan ta’adda suka gamu da ajalinsu bayan da suka kai wa sojojin hari.

Ma’aikatar Tsaron Cikin Gida da Harkokin Cikin Gida ta Jihar Katsina ta ce sojojin sun mayar da martani cikin gaggawa, suka fatattake su, suka kuma hallaka duka hudu ba tare da an samu asarar rai daga bangaren sojojin ba.

An kwato bindiga kirar AK-47 mai cike da harsasai biyar, babura guda biyu, wayoyin hannu da kuma tsabar kudi Naira N153,400 a hannunsu.

Tabbayyana cewa wasu daga cikin wayoyin da aka kwato na dauke da hotunan mutanen cikin kayan sojoji, kuma an mika su don bincike.

Binciken farko ya gano sunayen wadanda aka hallaka da suka hada da Bishir Holami, Jamilu Baki, Ibrahim Doro, da Abdurraman Maje.

Gwamnati ta bayyana su a matsayin manyan kwamandoji da ke da hannu a hare-haren da suka addabi al’ummomin Gobirawa, Raddawa, Kuki da sauran kauyuka a Dutsinma da Matazu.

Gwamnatin ta bayyana kashe su a matsayin babban cikas ga shahararren shugaban ’yan ta’adda, Muhammadu Fulani, wanda ake danganta da hare-haren ta’addanci a yankunan Matazu, Musawa, Charanchi da Kankia.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp