Home Taska NNPCL ya ƙulla Yarjejeniyar Kammala Gyaran Matatun Mai na Fatakwal da Warri

NNPCL ya ƙulla Yarjejeniyar Kammala Gyaran Matatun Mai na Fatakwal da Warri

NNPCL

NNPCL ya ƙulla Yarjejeniyar Kammala Gyaran Matatun Mai na Fatakwal da Warri

 

Kamfanin Man Fetur na Najeriya NNPCL ya rattaba hannu kan yarjejeniyar kammala aikin gyara matatun mai na Fatakwal da ke Jihar Ribas da kuma ta Warri da ke Jihar Delta.

Yarjejeniyar da NNPCL ɗin ya ƙulla da wasu kamfanonin China biyu domin kammala matatun na zuwa ne bayan gaza ƙarasa aikin da ya laƙume dala biliyan 2.39 a baya.

Sanarwar da kamfanin ya fitar ta ce yarjejeniyar za ta samar da abokan hulɗa da za su taimaka wajen farfaɗo da matatun da kuma bunƙasa harkokin sarrafa mai da masana’antun sinadarai.

Ko da yake gwamnati ta kashe biliyoyin daloli wajen gyaran matatun a baya, ciki har da wanda aka ce ya fara aiki a Fatakwal kafin ya sake tsayawa, har yanzu ba a bayyana adadin kuɗin da za a kashe a sabon shirin ba.

NNPCL ta bayyana matakin a matsayin wani muhimmin ci gaba na neman ɗorewar aiki da riba a matatun mai na ƙasar, tare da jaddada cewa ana ci gaba da tattaunawa kafin cimma cikakkiyar yarjejeniya.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp