Home Taska NNPCL ya ƙulla Yarjejeniyar Kammala Gyaran Matatun Mai na Fatakwal da Warri

NNPCL ya ƙulla Yarjejeniyar Kammala Gyaran Matatun Mai na Fatakwal da Warri

NNPCL

NNPCL ya ƙulla Yarjejeniyar Kammala Gyaran Matatun Mai na Fatakwal da Warri

 

Kamfanin Man Fetur na Najeriya NNPCL ya rattaba hannu kan yarjejeniyar kammala aikin gyara matatun mai na Fatakwal da ke Jihar Ribas da kuma ta Warri da ke Jihar Delta.

Yarjejeniyar da NNPCL ɗin ya ƙulla da wasu kamfanonin China biyu domin kammala matatun na zuwa ne bayan gaza ƙarasa aikin da ya laƙume dala biliyan 2.39 a baya.

Sanarwar da kamfanin ya fitar ta ce yarjejeniyar za ta samar da abokan hulɗa da za su taimaka wajen farfaɗo da matatun da kuma bunƙasa harkokin sarrafa mai da masana’antun sinadarai.

Ko da yake gwamnati ta kashe biliyoyin daloli wajen gyaran matatun a baya, ciki har da wanda aka ce ya fara aiki a Fatakwal kafin ya sake tsayawa, har yanzu ba a bayyana adadin kuɗin da za a kashe a sabon shirin ba.

NNPCL ta bayyana matakin a matsayin wani muhimmin ci gaba na neman ɗorewar aiki da riba a matatun mai na ƙasar, tare da jaddada cewa ana ci gaba da tattaunawa kafin cimma cikakkiyar yarjejeniya.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp