Home Taska NNPCL ya ƙulla Yarjejeniyar Kammala Gyaran Matatun Mai na Fatakwal da Warri

NNPCL ya ƙulla Yarjejeniyar Kammala Gyaran Matatun Mai na Fatakwal da Warri

NNPCL

NNPCL ya ƙulla Yarjejeniyar Kammala Gyaran Matatun Mai na Fatakwal da Warri

 

Kamfanin Man Fetur na Najeriya NNPCL ya rattaba hannu kan yarjejeniyar kammala aikin gyara matatun mai na Fatakwal da ke Jihar Ribas da kuma ta Warri da ke Jihar Delta.

Yarjejeniyar da NNPCL ɗin ya ƙulla da wasu kamfanonin China biyu domin kammala matatun na zuwa ne bayan gaza ƙarasa aikin da ya laƙume dala biliyan 2.39 a baya.

Sanarwar da kamfanin ya fitar ta ce yarjejeniyar za ta samar da abokan hulɗa da za su taimaka wajen farfaɗo da matatun da kuma bunƙasa harkokin sarrafa mai da masana’antun sinadarai.

Ko da yake gwamnati ta kashe biliyoyin daloli wajen gyaran matatun a baya, ciki har da wanda aka ce ya fara aiki a Fatakwal kafin ya sake tsayawa, har yanzu ba a bayyana adadin kuɗin da za a kashe a sabon shirin ba.

NNPCL ta bayyana matakin a matsayin wani muhimmin ci gaba na neman ɗorewar aiki da riba a matatun mai na ƙasar, tare da jaddada cewa ana ci gaba da tattaunawa kafin cimma cikakkiyar yarjejeniya.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp