Home Labarai ‘Yan Bindiga sun Kashe Fararen Hula 11 a Katsina

‘Yan Bindiga sun Kashe Fararen Hula 11 a Katsina

Taswirar Katsina
Katsina

‘Yan Bindiga sun Kashe Fararen Hula 11 a Katsina

’Yan bindiga sun kai harin ne bayan awanni kaɗan da jami’an tsaro suka kashe wasu ’yan ta’addan tare da nasarar dakile wani hari da suka kai.

Ma’aikatar Tsaron Cikin Gida da Harkokin Cikin Gida ta Jihar Katsina ta bayyana cewa ’yan bindigar sun gamu da ajalinsu ne a lokacin da wani shahararren jagorn ’yan bindiga mai suna Mohammadu Fulani yake jagorantar su zuwa manyan gadoji a Karamar Hukumar Kankia da nufin aikata laifi.

Kwamishinan Tsaro na jihar, Nasiru Mu’azu, ya yi ta’aziyya ga iyalan waɗanda abin ya shafa tare da yin Allah wadai da harin.

Da aka samu wannan bayani, al’ummar yankin suka sanar da jami’an tsaro, inda DPO na Kankia ya tattara jami’an tsaro kuma suka yi nasarar dakile harin.

Jami’an tsaro sun yi artabu da ’yan bindigar, inda suka kashe da dama daga cikinsu tare da kwato babura guda takwas da kuma shanun da aka sace, kuma suna hannun ‘yan sanda a halin yanzu.

A cewar kwamishinan, daga baya ’yan bindigar suka sake taruwa, suka kai hairn ramuwar gayya a kauyen Gwalgoro da ke cikin Gundumar Gyaza/Kunduru da misalin ƙarfe 12 na rana, inda suka kashe mazauna kauyen goma sha ɗaya a abin da gwamnati ta bayyana a matsayin “mugun hari kan fararen hula marasa laifi.”

Gwamnatin jihar ta tir da kisan, tana mai bayyana kai wa fararen hula hari a matsayin abin da ba za a taɓa yarda da shi ba kuma aikin ta’addanci ne.

Ta kuma yaba da gaggawar jami’an tsaro wajen dakile harin farko, tare da ƙarfafa mazauna yankin da su ci gaba da kasancewa cikin shiri da kuma bayar da bayanai cikin lokaci ga jami’an tsaro.

Haka kuma ta tabbatar da kudirin gwamnati na ci gaba da yaki da rashin tsaro da kare rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin jihar.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp