Home Labarai ‘Yan Bindiga sun Kashe Fararen Hula 11 a Katsina

‘Yan Bindiga sun Kashe Fararen Hula 11 a Katsina

Taswirar Katsina
Katsina

‘Yan Bindiga sun Kashe Fararen Hula 11 a Katsina

’Yan bindiga sun kai harin ne bayan awanni kaɗan da jami’an tsaro suka kashe wasu ’yan ta’addan tare da nasarar dakile wani hari da suka kai.

Ma’aikatar Tsaron Cikin Gida da Harkokin Cikin Gida ta Jihar Katsina ta bayyana cewa ’yan bindigar sun gamu da ajalinsu ne a lokacin da wani shahararren jagorn ’yan bindiga mai suna Mohammadu Fulani yake jagorantar su zuwa manyan gadoji a Karamar Hukumar Kankia da nufin aikata laifi.

Kwamishinan Tsaro na jihar, Nasiru Mu’azu, ya yi ta’aziyya ga iyalan waɗanda abin ya shafa tare da yin Allah wadai da harin.

Da aka samu wannan bayani, al’ummar yankin suka sanar da jami’an tsaro, inda DPO na Kankia ya tattara jami’an tsaro kuma suka yi nasarar dakile harin.

Jami’an tsaro sun yi artabu da ’yan bindigar, inda suka kashe da dama daga cikinsu tare da kwato babura guda takwas da kuma shanun da aka sace, kuma suna hannun ‘yan sanda a halin yanzu.

A cewar kwamishinan, daga baya ’yan bindigar suka sake taruwa, suka kai hairn ramuwar gayya a kauyen Gwalgoro da ke cikin Gundumar Gyaza/Kunduru da misalin ƙarfe 12 na rana, inda suka kashe mazauna kauyen goma sha ɗaya a abin da gwamnati ta bayyana a matsayin “mugun hari kan fararen hula marasa laifi.”

Gwamnatin jihar ta tir da kisan, tana mai bayyana kai wa fararen hula hari a matsayin abin da ba za a taɓa yarda da shi ba kuma aikin ta’addanci ne.

Ta kuma yaba da gaggawar jami’an tsaro wajen dakile harin farko, tare da ƙarfafa mazauna yankin da su ci gaba da kasancewa cikin shiri da kuma bayar da bayanai cikin lokaci ga jami’an tsaro.

Haka kuma ta tabbatar da kudirin gwamnati na ci gaba da yaki da rashin tsaro da kare rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin jihar.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp