Home Labarai ‘Yan Bindiga sun Kashe Fararen Hula 11 a Katsina

‘Yan Bindiga sun Kashe Fararen Hula 11 a Katsina

Taswirar Katsina
Katsina

‘Yan Bindiga sun Kashe Fararen Hula 11 a Katsina

’Yan bindiga sun kai harin ne bayan awanni kaɗan da jami’an tsaro suka kashe wasu ’yan ta’addan tare da nasarar dakile wani hari da suka kai.

Ma’aikatar Tsaron Cikin Gida da Harkokin Cikin Gida ta Jihar Katsina ta bayyana cewa ’yan bindigar sun gamu da ajalinsu ne a lokacin da wani shahararren jagorn ’yan bindiga mai suna Mohammadu Fulani yake jagorantar su zuwa manyan gadoji a Karamar Hukumar Kankia da nufin aikata laifi.

Kwamishinan Tsaro na jihar, Nasiru Mu’azu, ya yi ta’aziyya ga iyalan waɗanda abin ya shafa tare da yin Allah wadai da harin.

Da aka samu wannan bayani, al’ummar yankin suka sanar da jami’an tsaro, inda DPO na Kankia ya tattara jami’an tsaro kuma suka yi nasarar dakile harin.

Jami’an tsaro sun yi artabu da ’yan bindigar, inda suka kashe da dama daga cikinsu tare da kwato babura guda takwas da kuma shanun da aka sace, kuma suna hannun ‘yan sanda a halin yanzu.

A cewar kwamishinan, daga baya ’yan bindigar suka sake taruwa, suka kai hairn ramuwar gayya a kauyen Gwalgoro da ke cikin Gundumar Gyaza/Kunduru da misalin ƙarfe 12 na rana, inda suka kashe mazauna kauyen goma sha ɗaya a abin da gwamnati ta bayyana a matsayin “mugun hari kan fararen hula marasa laifi.”

Gwamnatin jihar ta tir da kisan, tana mai bayyana kai wa fararen hula hari a matsayin abin da ba za a taɓa yarda da shi ba kuma aikin ta’addanci ne.

Ta kuma yaba da gaggawar jami’an tsaro wajen dakile harin farko, tare da ƙarfafa mazauna yankin da su ci gaba da kasancewa cikin shiri da kuma bayar da bayanai cikin lokaci ga jami’an tsaro.

Haka kuma ta tabbatar da kudirin gwamnati na ci gaba da yaki da rashin tsaro da kare rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin jihar.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp