Home Taska Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto 

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto 

'Yan Bindiga

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto 

 

An samu rahoton kashe Babban Limamin ƙauyen Talluje da ke Ƙaramar Hukumar Bodinga a Jihar Sakkwato ranar Laraba, bayan da ’yan bindiga suka kai hari a Talluje da maƙwabtanta ƙauyen Chofi.

Lamarin ya yi sanadin mutuwar wasu mazauna ƙauyen guda biyu tare da tilasta wa ɗaruruwan mutane tserewa daga gidajensu.

Harin, wanda ya fara da misalin ƙarfe 4:00 na yamma, ya auka wa unguwanni biyu da ke Gundumar Danchadi, kuma ya shafe kusan sa’o’i biyu ana fafatawa.

Wannan lamari ya kawo adadin sanadin rasa rayukan Manyan limamai guda uku da rahotanni suka ce ’yan bindiga sun kashe a Jihar Sakkwato cikin ‘yan makonnin da suka gabata.

Majiyoyi daga yankin sun shaida wa wakilinmu cewa, maharan sun kai hare-hare na bai-ɗaya a lokaci guda a duka unguwanni biyu, inda suka riƙa harbi ba ƙaƙƙautawa kafin su tsere da adadin dabbobin da ba a tantance ba waɗanda suka sace.

“Hare-haren sun fara ne da misalin ƙarfe 4:00 na yamma kuma suka ci gaba har zuwa kusan ƙarfe 6:00 na yamma. ’Yan bindigar sun kashe Babban Limamin Talluje da wasu mutane biyu waɗanda har yanzu ba a tantance ko su wane ne ba,” in ji wani shugaban unguwa a Danchadi.

Ya ƙara da cewa, hare-haren sun haddasa gudun hijira, inda mazauna yankin, musamman mata da ƙananan yara, suka tsere da ƙafafunsu zuwa wurare mafi aminci a Danchadi da garin Bodinga.

“Yayin da nake magana da kai, mutane da yawa suna tserewa daga unguwanninsu ɗauke da kayayyakinsu bayan sun tsere daga asalin ƙauyukan da abin ya shafa,” in ji majiyar.

Wani mazaunin yankin ya tabbatar da cewa, maharan sun kwashe dabbobi masu yawa, kodayake ba a iya tantance ainihin adadin su ba nan take.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Labarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu MohammedJami'an Tsaro Sun Kai Farmaki Sansanin IPOB/ESN, Sun Kawar da 'Yan Ta'adda 6 a AnambraOperation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Lalata Motocin Yaƙi Guda Biyu na ISWAP, Sannan Ya Kawar da Ƴan Ta'adda da Dama a BornoMai fafutuka Mahdi Shehu ya yi Gargadin Cewa Kudirin Dokar NGO Zai iya Shafar Masallatai, Coci, da Ƙungiyoyin ɗalibaiRikicin Karkashin Mulkin APC a Katsina: ADC na Radda da CSO Har Yanzu Suna Tsare a Hannun Masu ba Tinubu Shawara, MasariAnambara: Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'addan IPOB/ESN, Sun Kwato MakamaiHukumar Kwastam ta Kano ta Mika Magungunan da ba a yi wa Rijista ba ga NAFDAC, ta Kuma yi Alƙawarin Tsaurara Matakan Aiki.Operation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Kawar da 'Yan Ta'adda 36 a BornoFamadewa, Ribadu da Shirin Tsaron Kwanaki 90: Yadda YAShuaib ya Binciki Sanarwar OnanugaLabarin NIPSS Ya Bayyana Cin Zarafin Babban Jami'in Sojan Ruwa, Rear Admiral AA MustaphaƊaliban PRNigeria Sun Yaba da Gyare-Gyaren FRSC, Sun Nemi Ƙarin Ƙarfafa Sadarwa Kan Tsaron HanyaYadda Dalibai 4 Almajirai Suka Mutu Bayan Cin Kife da Ake Zargi da Guba a KanoSojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Sace a Dajin KatsinaTinubu Ya Nada Abel Enitan A Matsayin Sabon Shugaban Ma'aikatan Tarayya
X whatsapp